24
Apr
NASIHA
Posted April 24, 2011 by iyalina in Fagen Nishadi. 1 Comment
-
“Iyaye su shayar da ‘ya’yansu shekaru biyu cif-cif ga wadanda suka nufi
cika lokacin shayarwa” (Bakara : 233).
- Annabi (SAW)
ya ce: “Ku umarci ‘ya’yanku da su yi sallah suna ‘yan shekara bakwai, in suka
kai goma ba su yi ba, ku doke su a kanta, kuma ku raba musu makwanci” (Abu
Dawud).
- Annabi (SAW)
ya ce: “In mutum yana so ya zama tantagaryar makaryaci, to duk abin da ya ji ya
karas (Muslim).
- Bincike ya nuna cewa iya yawan haddace-haddacen da mutum yake yi, iya kara fadin da kwakwalwarsa take yi da
kara rike abubuwa.
Like this:
Be the first to like this post.
Posted by HABIBU SHEHU ABDULLAHI on June 7, 2011 at 11:35 am
Nasiha ta garemu duka shine mu tsaya, tsayuwar daka mu kyautata zamantakewarmu a bisa tsari irin na musulunci kamar yadda muka ga iyayenmu sun kokarin dabbakawa a cikin rayuwarsu ta yau da kullum. Kuma wannan ne tasa ake kallonsu da kima da nagarta, ba kamar yadda muke gudanar da rayuwarmu a yanzu ba. Son yaya, dukiya, mata da zuciya ta samu a cikin wannan kaka ni kayi. Allah kayi mana gudunmawa a bisa gyaran wannan al’umma. Amin.