“Ku kyautata Allah yana son Masu kyautatawa” (Bakara: 195)
¨ “Wanda ba ya girmama manyanmu,kuma ba ya tausayin kananamu ba
shi daga cikinmu” (Sahihul Jami’a)
¨ Annabi (SAW) ya ce: “Ku rika musayen kyuta (a junanku) sai soyayyar
(dake tsakaninku) ta karu.(Sahihul Al’adabul Mufrad)
¨ Annabi (SAW) yana ziyartar ‘ya’yansa a gidajen mazansu. Kai ma ka rika yin haka nan, sai ka dace da sunna, kuma soyayyar dake tsakaninku ta kara habaka.
Allah yana son Masu kyautatawa
SHAWARWARI!!!
Aljanna tana karkashin dugadugan mahaifa (mata) (Ahmad da Nasa’i)
• Don isar da sakon nasiha, ga mijinki,ko mahaifinki rika ajiye masa KASET din da ya kunshi wannan sakon A CIKIN MOTA kusa da wurin sa kaset (ba tare da kin gaya masa ba)
• Annabi (SAW) yakan taya matansa aikin gida.
• Me kake so ka zama a nan gaba?
• Kyautatawa danka yana karami,sai ya kyutata maka in ya girma
RIKA AIKAWA DA KAWAYENKI WADANNAN SAKWANNI TA WAYA !!!
Tsoron Allah shi ne tushen nasara a zamantakewar aure da tarbiyyah.
“Kar ku manta da mutuncin dake tsakaninku (Bakara:237 ) .
Namiji da bangaren HAGU na kwakwalwarsa yake tunani, mace kuma na DAMA. Ya za ki amfana da wanan bayanin a zamanki da mijinki?
Zama baiwar mijinki, sai ya zama bawanki
“Idan muslumi ya ciyar da iyalinsa don neman lada a wurin Allah, ta zama sadaka (Bukhari: 5351).
Gangancin yaro kuskure ne.
Wanda ya wahala yana yaro, in ya girma zai huta.