Allah yana son Masu kyautatawa

“Ku kyautata Allah yana son Masu kyautatawa” (Bakara: 195)
¨ “Wanda ba ya girmama manyanmu,kuma ba ya tausayin kananamu ba
shi daga cikinmu” (Sahihul Jami’a)
¨ Annabi (SAW) ya ce: “Ku rika musayen kyuta (a junanku) sai soyayyar
(dake tsakaninku) ta karu.(Sahihul Al’adabul Mufrad)
¨ Annabi (SAW) yana ziyartar ‘ya’yansa a gidajen mazansu. Kai ma ka rika yin haka nan, sai ka dace da sunna, kuma soyayyar dake tsakaninku ta kara habaka.

Published in:  on May 6, 2009 at 12:42 pm Leave a Comment

SHAWARWARI!!!

Aljanna tana karkashin dugadugan mahaifa (mata) (Ahmad da Nasa’i)

 • Don isar da sakon nasiha, ga mijinki,ko mahaifinki rika ajiye masa KASET din da ya kunshi wannan sakon A CIKIN MOTA kusa da wurin sa kaset (ba tare da kin gaya masa ba)

• Annabi (SAW) yakan taya matansa aikin gida.

• Me kake so ka zama a nan gaba?

 • Kyautatawa danka yana karami,sai ya kyutata maka in ya girma

Published in:  on May 5, 2009 at 6:26 am Leave a Comment

RIKA AIKAWA DA KAWAYENKI WADANNAN SAKWANNI TA WAYA !!!

Tsoron Allah shi ne tushen nasara a zamantakewar aure da tarbiyyah.
“Kar ku manta da mutuncin dake tsakaninku (Bakara:237 ) .
Namiji da bangaren HAGU na kwakwalwarsa yake tunani, mace kuma na DAMA. Ya za ki amfana da wanan bayanin a zamanki da mijinki?
Zama baiwar mijinki, sai ya zama bawanki
“Idan muslumi ya ciyar da iyalinsa don neman lada a wurin Allah, ta zama sadaka (Bukhari: 5351).
Gangancin yaro kuskure ne.
Wanda ya wahala yana yaro, in ya girma zai huta.

Published in:  on at 6:11 am Leave a Comment