ALLAH YA GAFARTA WA WANCE !!!

Imamu Ahmad (Allah ya ji kansa) bai yi auren fari ba sai da ya kai shekara arba’in; da ya tashi aure sai ya fara tantance gidan da ya kamata ya hada zuriya da su, sai aka ce masa akwai ‘yan mata biyu a gidan, daya kyakkyawa ce, dayar kuma idonta daya, sai ya ce wacce ta fi hankali? sai aka ce mai ido dayan, sai ya ce: ita za ku aura min. Zamansu ya yi dadi sosai. Bai yi wani auren ba sai da ta rasu.

 Yake cewa: Almarwazi daya daga cikin daliban imamu Ahmad (Allah ya ji kansa) ya ce: wata rana imamu Ahmad ya ambaci iyalinsa bayan ta rasu sai ya ce: Allah ya gafarta wa wance, shekararmu ashirin tare amma ko sabani ba mu taba ba.

 

Published in:  on March 27, 2009 at 8:24 pm Leave a Comment

The URI to TrackBack this entry is: http://iyalina.wordpress.com/2009/03/27/allah-ya-gafarta-wa-wance/trackback/

RSS feed for comments on this post.

Leave a Comment