ALLAH YA GAFARTA WA WANCE !!!

Imamu Ahmad (Allah ya ji kansa) bai yi auren fari ba sai da ya kai shekara arba’in; da ya tashi aure sai ya fara tantance gidan da ya kamata ya hada zuriya da su, sai aka ce masa akwai ‘yan mata biyu a gidan, daya kyakkyawa ce, dayar kuma idonta daya, sai ya ce wacce ta fi hankali? sai aka ce mai ido dayan, sai ya ce: ita za ku aura min. Zamansu ya yi dadi sosai. Bai yi wani auren ba sai da ta rasu.

 Yake cewa: Almarwazi daya daga cikin daliban imamu Ahmad (Allah ya ji kansa) ya ce: wata rana imamu Ahmad ya ambaci iyalinsa bayan ta rasu sai ya ce: Allah ya gafarta wa wance, shekararmu ashirin tare amma ko sabani ba mu taba ba.

 

Published in:  on March 27, 2009 at 8:24 pm Leave a Comment

MAKKA BABBAN GARI HAR DA GONAR LANTARKI!!!

In ji wani dan Fulani lokacin da yaje kasa mai tsarki domin yin aikin hajji bayan jirginsu ya sauka a filin jirgin sama na sarki AbdulAziz dake Jidda (kasancewar akwai fitulu da dama akan doron titin filin jirgin).

Published in:  on at 8:10 pm Leave a Comment

AN YI MUSU BUSHARA DA ALJANNA TUN SUNA DUNIYA !!!

SUNAYEN SAHABBAI GOMA DA AMBATONSU YA ZO A HADISI GUDA AKA YI MUSU BUSHARA DA ALJANNA TUN SUNA DUNIYA:

1. Abubakar Assiddik ( Allah ya yarda da shi).

2. Umar Alfaruq (Allah ya yarda da shi).

3. Usman Ibn Affan (Allah ya yarda da shi).

4. Aliyu Ibn Abi Dalib (Allah ya yarda da shi).

5. Abu Ubaida Ibnul Aljarrah (Allah ya yarda da shi).

6. Abdul Rahman Ibnu Auf (Allah ya yarda da shi).

7. Azzubair Ibnul Awwam (Allah ya yarda da shi).

8. Dalhatu Ibnu Ubaidillah (Allah ya yarda da shi).

9. Sa’ad Ibnu Abi Wakkas (Allah ya yarda da shi).

10. Sa’id Ibnu Zaid (Allah ya yarda da shi).

 

Published in:  on at 7:08 pm Leave a Comment