An karbo daga Abu Qatada Al-ansari Allah ya yarda dashi ya ce;An tambayi Annabi Muhammad [S.A.W] akan Azumin ranar Arafa,sai yace;”yana kankare zunuban shekara biyu,shekarar da ta wuce da shekarar dake gabarta”.Sai kuma aka tambaye shi akan azumin ashura,sai yace”yana kankare zunuban skakarar da ta wuce”,sannan aka kara tambayar shi akan azumin ranar litinin sai yace;”wannan shine ranar da aka haife ni,ranar da aka turo ni,kuma shine ranar da aka saukar mini da wahayi”
Muslim ne ya rawaito.
Alqasim Ahmad Elnafaty