‘Yan uwana matasa Ina yi muku fatan alheri da sallama ta muslunci; Assalamu
alaikum. Bayan haka:
Saninmu ne mu matasa cewa akwai mu da son kwaikwayo da daukar salo na wasu fitattu a fagage daban daban, kamar ’yan bal, ’yan fim, makada, da mawaka dss. Amma idan muka tsaya muka yi tunani yadda ya kamata, za mu ga ba mu da taurarin da suka fice matasan magabatanmu na kwarai da suka shude; kamar Annabawa lokacin suna matasa, matasan sahabbai, da na tabi’ai dss. Idan muka dubi irin su Annabi yusuf, Nana Maryam, Nana A’isha, Aliyyu ibn Abi dalib, Ibn Abbas Allah ya yarda da su baki daya za mu ga ba karamar nasara suka ci ba a rayuwarsu, don haka sai mu bi hanyar da suka bi. A fitowa ta gaba in sha Allahu zan ba ku labarin wani matashi daga cikin sahabbai wanda nasarar da ya samu a rayuwarsa ta kai ya zama abokin sirrin manzon Allah (SAW) kuma dan aljanna tun yana duniya.
Khadija Muhammad Kabir Yunus