Rana zafi Inuwa Kuna

Wata rana na bakunci gidan wani mutum sai ya fito mana da abinci kamar yadda al’adar girmama bako take wurin bahaushe, can sai dansa ya fito yana kuka wurjanjan, ganinsa ke da wuya sai ya kama fada yana cewa yaran nan kawai su su zo su hana mutane sakat! sai kawai ya daga hanu ya dalla masa mari ya ce tafi ka ba ni wuri, sai yaron ya yi kamar zai ruga wurin uwarsa cikin gida, amma sai ya yi turus; ya rasa inda za shi, ashe uwarsa ce ta fara zabga  masa mari ya taho wurin uban ko  ya samu sauki amma ina? ai wannan shine an yi gudun gara an tadda zago, ko in ce “Rana zafi inuwa kuna” ‘yanuwana mahaifa Annabi (SAW) yana cewa: “Tausasawa ba ta taba kasancewa a cikin abu ba sai ta adonta shi, ba’a kuma zare ta daga cikin abu ba sai ya yi muni”

Hamza Aliyu Sakwaya

 

Published in:  on May 16, 2008 at 2:13 pm Leave a Comment

Hukuncin Aure a Musulunci

Aure a karan kan sa halal ne, musamman ga wanda ke da sha’awa da iko; Sunna ce ta Manzannin Allah; Haka kuma, Manzo SAW ya yi aure, sannan kuma ya ce: ((Lalle ni ina auren mata, don haka duk wanda ya kyamaci sunnata, to ba ya tare da ni))

Don haka ne malamai su ka ce: “aure ya fi ayyukan nafila, ga wanda ke da sha’awa, domin shi ya kunshi ayyukan alheri da dama”.

Amma kuma a wasu lokuta, aure kan zama wajibi, kamar ga mutumin da ke da tsananin sha’awa kuma ya ke tsoron fadawa  cikin haramun idan bai yi auren ba. A nan, ya zama wajibi ya yi auren don kada ya fada cikin haram.

Published in:  on May 7, 2008 at 7:34 pm Leave a Comment

Dukkaninku Makiyaya ne

Annabi (SAW) y ace: ” Kowa ya saurara ya ji: Dukkaninku masu kiwo ne, kuma kowanneku sai an tambaye shi kiwon da aka ba shi… Namiji makiyayi ne game da mutanen gidansa, kuma sai an tambaye shi akan abin da aka ba shi kiwo, mace ma makiyiya ce a gidan mijinta, da ‘ya’yansa, kuma sai an tambaye ta akansu… (Buhari da Muslim)

Published in:  on at 7:29 pm Leave a Comment

Tambaya 0004

Tambaya: Mene ne matsayin aske gashin kai ga mace ba tare da dalili ba? Kuma menene hukuncin }arin gashi?

**Maryam Husain Falaki

 Amsa: Gashi ado ne ga mace da Allah (SWT) ya ba ta, hukuncin aske gashi ga mace na da halaye guda uku:

1-Ta aske shi saboda wata masifa ta faru a gareta kamar mutuwa da waninta, wannan haramun ne; domin Annabi (SAW) ya ce: ba shi ba matar da take aikata haka, kamar yadda Imam Bukhari da Imam Muslim suka rawaito daga hadisin Abu Musa Al’ash’ari Allah ya yarda da shi.

2-Ta aske shi domin wata larura kamar rashin lafiya. A wannan hali tana da damar yin haka, babu mai a kanta.

3-Ta aske shi ba tare da wata larura ba, mafi yawan malamai suna ganin cewa wannan laifi ne, ba ya halatta, domin canza kama ne. Gameda matsayin }arin gashi a musulunci kuwa? Amsa ita ce: Baya halatta ga mace ta }ara gashinta. babu bambanci wurin haramci tsakanin gashin mutum da waninsa, ya tabbata a cikin hadisai da dama Annabi (SAW) ya la’anci mace mai }ara gashinta.

 Allah Shi ne mafi sani.

 Dr. Muhd. A. Abubakar

 

Published in:  on May 3, 2008 at 10:05 pm Leave a Comment