Daga cikin amfanin da na gari

Annabi (SAW) ya ce: “Idan mutum ya rasu duk wani aikinsa ya yanke sai abubuwa uku: Sadaka mai gudana, ilimi mai amfani, da kuma DA NA GARI DA ZAI RIKA YI MASA ADDU’A”

Don haka iyaye sai a dage wurin tarbiyyantar ‘ya’ya tarbiyya ta gari.

 

Published in:  on May 29, 2008 at 8:24 pm Leave a Comment

Mahimmancin Sadazumunci

Annabi (SAW) ya ce: “Wanda duk yake so ya samu yalwar arzuki, da tsowon kwana, to ya sa da zumuncinsa” (Bukhari: 1555)

 

Published in:  on May 26, 2008 at 11:56 am Leave a Comment

Hadarin Shirka

Allah (SWA) ya ce:

“Hakika Allah ba ya gafarta a yi shirka da shi, amma yana gafarta abin da bai kai shirka ba ga wanda ya so, hakika wanda ya yi shirka da Allah ya kirkiri laifi mai girman gaske” (Sutarul Nisa’i: 48)

Published in:  on at 11:46 am Leave a Comment

Tasirin Tsine wa ‘ya’ya

Wani mutum ya kai kukan wani daga cikin ‘ya’yansa ga Abdullahi ibn Mubarak (R) , sai Abdullahi ibn Mubarak ya ce: “Ka tsine masa ne?” sai ya ce: “Gaskiya na tsine masa!” sai ya ce: “To ai kai ka bata shi!”   

Published in:  on May 23, 2008 at 3:35 pm Leave a Comment
Tags: ,

Dana yana zagi na a gaban baki ya zan yi da shi

Yana daga cikin abubuwan da yara suke samun kansu a ciki, yayin matakin yarinta   shine dabi`ar zagi, kuma wannan dabi`ar takan samu ne sakamakon wasu abubuwa da suke bujurowa yaro a wannan mataki da yake ciki, don haka wannan yaron a bisa yadda akayi bayani zagin bai zamo masa dabi`a ba, ta yadda ko yaushe yake yinsa, sai dai kawai yana yinsa ne a wani guri mai matukar girman gaske, don haka sai a bi wadannan matakan kamar haka :

 

1- Lallai ne a samu lokaci a ringa zama da wannan yaron domin kokarin sanin abubuwan da suke damunsa, da kuma kokarin nuna masa baci da munin wannan dabi`a da yakeyi yayin da yaga baki a gidansu.

2- A wannan mataki da yara suke ciki sukan so suyi wani abu da zasu ga sun birge ko a yabesu ko kuma suja hankalin mutane zuwa garesu, musamman ma idan yaga bako, dan haka zai iya yin wannan mummunar dabi`ar domin cimma daya daga cikin wadancan abubuwan da aka ambata, dan haka sai iyaye su yi kokarin saita yaro ta yanda zai kosar da kishinsa da abubuwa masu kyau .

3- Akan sami wasu yaran basa son suga baki ko kuma a je dasu wajan baki, dan haka da zarar anyi baki a gidansu, ko ya sami kansa a gurin baki to zai yi wani abu da Malaman Tarbiyya suke ce masa ( daukan fansa a matakin yarinta) don haka sai yaga menene zai yi wanda yasan bai kyauta ba, saboda ya huce fushinsa da damuwar da yake ciki sakamakon halin da ya samu kansa a ciki, don haka sai iyaye suyi kokarin cusa wa yaro son baki a zuciyar sa, da kuma bin duk wata hanya da ta dace da hankalinsa da kuma shekarunsa .

4- Yana da matukar amfani ya kasance duk ranar da akayi baki ko ya samu kansa cikinsu kuma bai yiwa babarsa abinda ya saba yi mata ba, to ta samu wani abu da tasan yana tsananin sonshi ta bashi shi kyauta, kuma lallai ne ta gaya masa dalilin da yasa ta yi masa wannan kyautar,

Wadannan sune yan shawarwarin da nake ganin zasu iya yin amfani, kuma lallai ne iyaye maza su ringa shiga irin wannan matsalar domin su taya iyaye mata tarbiyyar yaransu, domin alhakin kula da kuma tarbiyyar yara bawai a wuyan iyaye mata kadai yake ba, kamar yadda ya zama wajibi iyaye su tsaftace bakunan su daga irin wadannan munanan dabi`u, domin yara sukan koyi abubuwa da yawa a wajan iyayensu .

Allah ya sa mu dace,

Dr. Ibrahim Abdullahi Sani R\lemo  

 

Published in:  on May 21, 2008 at 2:08 pm Leave a Comment

Wasiyyar Qais Ass’ady (R.A) ga ‘ya’yansa

Lokacin da  Qais ibn Asim Assa’dy (RA) -daya daga cikin Sahabbai– yake cutar ajali, ya tara  ‘ya’yansa  ya ce musu: “Ku yi  aiki da abin  da zan gaya muku; don ba wanda za ku yi aki da maganarsa da ya fi ni son ya gaya muku abin da zai amfane ku. Idan  na cika kada ku yi min kururwa; don na ji Annabi (SAW) yana hana a yi wa mamaci ihu,  kuma shi ma da ya rasu ba’a yi masa ihu ba, ku yi min likkafani da kayan da nake sallah da su, ku shugabantar da manyanku … ku nemi na-kanku, don ku wadatu daga mutane, ba ku ba maula; don maula ita ce hanya mafi kaskanci da mutum zai bi don samun na abinci…”   

 

 

Published in:  on at 2:02 pm Leave a Comment

Tsallan Badake

Badake wani mutum ne da ya ga samu ya ga rashi, ko kuma a ce “ya bata rawarsa da tsalle” Yadda abin kuwa ya faru shi ne: ani sarki ne yake da wata ‘ya “Son kowa kin wanda ya rasa” ya ce ba zai aurawa kowa ba sai wanda ya tsallake wata tsohuwa, kuma wawakekiyar rijiya. Samari suna ta gwadawa amma kowa sai a dauko shi tsamo-tsamo. Rannan sai Badake ya zo ya gwada sa’arsa, aka yi ta yi masa washi, da kirari “Badake Badake!! Badake!!!, da kansa ya gama fasuwa, kawai sai ya zabura, ya sheko aguje, firrr kamar tsuntsu, ya shallake rijiyar nan! Sai aka yi ta iho, ana sowwa, ana yi masa tafi, ana kuma tila masa kasa, sai Badake ya fara cika baki yana cewa: dama wannan ’yar rijiyar ce don abin kunya kwana da kwanaki aka rasa mai tsallake ta! to ni ko da baya da baya ba sai in tsallake ta ba! Sai wasu suka ce gafara nan kai din me! wannan din ma sa’a ka yi! Kawai Badake sai ya tashi a fusace, ya nufi rijiya da baya da baya, su kama ’yan zuga sai ihu suke yi; Badake!, Badake!!. Badake ya taho da gudu da baya zai tsallake rijiya, sai ZUNDUUUM!!! ya fada” shi kenan ya ga samu ya ga rashi! Shi ya sa wanda ya samu kansa a makamancin halin wannan mutum sai a ce “ya yi tsallaen Badake. To, “ Allah ya kiyaye mu da tsallen Badake”

Published in:  on May 20, 2008 at 2:51 pm Leave a Comment

Hukuncin karin gashi

Tambaya: Mene ne matsayin aske gashin kai ga mace ba tare da dalili ba? Kuma menene hukuncin karin gashi?

Maryam Husain Falaki

 Amsa: Gashi ado ne ga mace da Allah (SWT) ya ba ta, hukuncin aske  gashi ga mace na da halaye guda uku: 1-Ta aske shi saboda wata masifa ta faru a gareta kamar mutuwa da waninta, wannan haramun ne; domin Annabi (SAW) ya ce: ba shi ba matar da take aikata haka, kamar yadda Imam Bukhari da Imam Muslim suka rawaito daga hadisin Abu Musa Al’ash’ari Allah ya yarda da shi. 2-Ta aske shi domin wata larura kamar rashin lafiya. A wannan hali tana da dammar yin haka, babu komai a anta. 3-Ta aske shi ba tare da wata larura ba, mafi yawan malamai suna ganin cewa wannan laifi ne, ba ya halatta, domin canza kama ne. Gameda matsayin karin gashi a musulunci kuwa? Amsa ita ce: Baya halatta ga mace ta kara gashinta. babu bambanci wurin haramci tsakanin gashin mutum da waninsa, ya tabbata a cikin hadisai da dama Annabi (SAW) ya la’anci mace mai kara gashinta. Allah Shi ne mafi sani.  

 

 

Dr. Muhd. A. Abubakar

 

Published in:  on at 2:33 pm Leave a Comment

Adadin Matan da ya halatta a Aura

Saboda kasancewar kyale mutum ya auri mata iya adadin da ya ga dama ba tare da iyaka ba, abu ne da zai iya kaiwa ga rudani, zalunci da rashin kula da hakkokin matan; Kuma saboda takaita mutum ga mace guda kadai zai iya kaiwa ga kokarin biyan bukatar sha’awarsa ta hanyar da a ka haramta; Musulunci ya halatta mutum ya auri mata har zuwa hudu, domin wannan shi ne iyakar adadin matan da mutum zai iya kayiye adalci tare da kula hakkokin matan, idan har ya na bukatar mace fiye da daya.

Fa’idar auren fiye da mace daya ta hada da:

  1. Wasu lokutan ya kan zama dole a yi haka kamr idan matar ta kasance tsohuwa ko ba ta da lafiya kuma idan ya hakura da ita ba zai iya kame sha’awarsa ba, kuma su na da ‘ya’ya tare da ita. Ke nan, idan ya ci gaba da zama da ita kadai, ya na tsoron fadawa  cikin sabon Allah game da sha’awarsa, kuma idan ya sake ta, zai raba ta da ‘ya’yanta. Don haka wannan matsala ba ta da wani magani sai auren mace fiye da daya.
  2. Aure wata hanya ce ta samar da alakoki tsakanin al’ummomi da yawa don haka auren mata da yawa na fadada alakoki tsakanin gidaje da dama da al’ummomi, don haka ne ma Manzon Allah (SAW) ya auri mata da dama. .
  3. Auren mata fiye da daya ya na bayar da kariya gare su ta hanyar samar da bukatunsu na ci da sha da makwanci da sha’awa da haihuwa da sauran manufofin Shari’ar Musulunci.
  4. A cikin mazaje akwai wadanda ke da karfin sha’awa ta yanda mace guda ba za ta iya biya masu bukatunsu ba, ko da kuwa sun kasance masu imani da tsoron Allah, kuma ba sa son fadawa  cikin zina, kuma su na so su biya bukatarsu ta hanyar da Shari’ah ta halatta. Don haka, sai Allah, cikin RahamarSa, ya halatta ma su samun mace fiye da daya ta hanya amintacciya.

Sheikh Ibn Uthaimin

Published in:  on May 16, 2008 at 3:10 pm Leave a Comment

Matan da ya haramta a aura

Matan da ya haramta a aura sun kasu kashi biyu:

(1) Wadanda su ka haramta har abada – su ne:

(A) Mata bakwai (7) wadanda a ka haramta saboda dangantaka ta jini da mijin: kamar yanda ya zo a Suratun Nisa’i aya ta aya ta 23, kamar haka:

(i) Uwayewato mahaifya da kakanni mata ta bangarorin uwa da uba, ko mai nisansu; (ii)’Ya’ya mata – wato ‘yar mutum ta cikinsa da ‘yar dansa ko ‘yarsa, kome nisansu; (iii) ‘Yar uwa – wa ya ko kanwa, uwa daya uba daya, ko uba daya, ko uwa daya;(iv) Gwaggwanni – wato ya ko kanwar uba, da kuma gwaggwannin babansa, da babarsa da kakanninsa (maza da mata); (v) Innoni/Yakumbo – wato ya ko kanwar uwa, da kuma innonin mahaifinsa da mahaifiyarsa da kakanninsa (maza ko mata); (vi) ’Ya’yan ‘Yan uwa maza – wato ‘yar wansa ko kaninsa (uwa daya uba daya, ko uba daya, ko uwa daya) da kuma ‘ya’yan ‘yayansu maza ko mata dss; (vii) ’Ya’yan ‘Yan uwa mata – wato ‘yar yarsa ko kanwarsa (uwa daya uba daya, ko uba daya, ko uwa daya) da kuma ‘ya’yan ‘yayansu maza ko mata dss.

 (B) Mata bakwai (7) wadanda a ka haramta saboda shayarwa: Su ne wadanda su ka haramta a sama kamar yanda Manzon Allah (SAW) ya ce: ((Shayarwa na haramta duk abin da dangantakar jini ke haramtawa)) da sharadin: (i) Yaron ya sha nonon matar (sha na koshi) a kalla sau biyar, (ii) kuma dukkanin shayarwar ta faru ne kafin yaye.

Idan wadannan sharudda sun cika, to yaron ya zama dan wannan mata, kuma ‘ya’yanta sun zama ‘yan uwansa, ko da an haife su kafin ko bayan shayar da shi. Haka kuma, dukkan ‘ya’yan mijin da take shayar da dansa lokacin shayarwar sun zama ‘yan uwansa ko da daga wata matar suke ba ita ba. Amma ya kamata a lura a nan cewa, ‘yan uwan wanda a ka shayar din banda ‘ya’yansa, ba su da wata alaka da wannan shayarwar da hukun-hukuncenta. Don haka, ya halatta ga dan uwansa na jini ya auri matar da ta shayar da shi ko ya auri ‘yan uwarsa ta shawayarwa. Sai dai kuma ‘ya’yan dan da a ka shayar sun zama ‘ya’yan matar da ta shayar da shi da kuma uban dan da ta ke shayarwa a daidai lokacin da ta shayar da shi…

(C) Mata Hudu (4) wadanda a ka haramta saboda aurataiya: Su ne kamar haka:

 (i) Matan Uba wato matan mahaifinsa da kakansa (na uwa na uba) komai nisansa. Kuma da zarar an daura aure tsakanin mutum da wata mata, to ta haramta ga ‘ya’ayansa komai nisansu, ko da bai tare da ita ba. (ii) Matan ‘Ya’ya wato matan ‘ya’yansa komai nisansu, da sharadin dan ya tare da matar. (iii) Babar Matarsa wato mahaifiyar matarsa da kakarta, komai nisanta. Don haka, da zarar mutum ya auri mace, to babarta da kakanninta (na uwa da na uba) sun haramta gareshi, ko da bai tare da ita ba, komai nisan kakannin. (iv) ‘Ya’yan Matarsa da ‘ya’yan ‘ya’yansu (maza ko mata) da kuma jikanninsu komai nisansu, matukar dai ya tare da mata. Amma da saki ya afku kafin ya tare da matar, to wa]annan ‘ya’ya da ‘ya’yansu ba sa haramta gare shi, sawa’un an haife su kafin ko bayan ya aure ta.

 (2) Matan da su ka haramta a aure su zuwa wani lokaci – su ne:

 (A) ’Ya ko Kanwar Matarsa ko Goggonta wato na bangaren uwa ko uba har sai lokacin da su ka rabu da ita kodai ta rasu ko kuma bayan ya sake ta kuma ta kare idda.

(B) Matar da ke cikin Idda har sai ta kare iddar.

(C) Matarsa da ta shiga Harama – har sai ta kare aikin Hajji ko Umarar.

Sheikh Ibn Uthaimin

Published in:  on at 3:07 pm Leave a Comment