Assalamu alaikum. ‘Yan uwana yara zan ba ku tarihin wata babbar mata cikin iyayen muminai. Sunanta Khadijah bintu Khuwailid. Ita ce farkon matan Annabi (S A W) Ita ce farkon wadda ta fara muslinta, Ita ce kuma ta haifawa Manzon Allah (S A W) duka ‘ya yansa ban da Ibrahim. ‘Ya’yan nata su ne: 1) Abdallah, 2)Alqasim, 3) Zainab, 4) Rukayya, 5) Ummu kalsum, 6) Fadima. Yanzu ina so wani ko wata ta ba mu tarihin wata Sahabiyar a takaice kamar yadda ni ma na takaita.
Amina M. Muslim.