Yaushe dubu daya take daidai da milyan daya?

Wata rana wani matashi ya dawo gida sai ya ga tarin jama’a a kofar gidansu, gabansa ya yanke ya fadi; ya dauka ko rasuwa aka yi, daga baya sai ya ga ashe wai kannensa biyu mata ake daurawa aure, bai san ma an ba da su ba ballantana daurin aurensu! da ya yi magana sai aka ce masa: “To in an gaya maka me za ka iya yi?!” bai san lokacin da hawaye ya fara shatato masa ba, ya fito waje hawaye shabe-shabe yana cewa: “Allah ya raba mu da talauci!”

Bugu da kari, wata baiwar Allah ita ma ta koka da yadda mahaifanta suke watsi da ita, saboda mijinta ya talauce! Ta ce ada da suke da abin hannunsu, komai sai abin da ta ce a gidansu, musamman ma ga shi ita ce babba a gidan, amma da “yau” ta ci su da yaki sai ya zamana, wani lokaci ko sa ranar kannenta da suke ciki daya sai dai ta ji a sama! Ta ce wannan abu yana damuna fiye da misali, a ce talauci ya zabge mata daraja haka a idon iyayenta! Shi kuma wannan wani karamin ma’aikaci, kwatsam sai ya bar wannan aiki ya buge da wata kaskantacciyar sana’a da yake zaton zai yi saurin samun kudi ta ita, da aka tambaye shi, sai ya ce, ya yi haka ne saboda gudin fiushin mahaifiyarsa, saboda kannensa da yayyensa duk mawadata ne, don haka idan sha’ani ya taso– kamar biki ko suna– su kan ba ta kudi da yawa, shi kuma abin da yake iya ba ta bai taka kara ya karya ba, ita kuma sai ta yi ta fada har barazanar tsine masa take yi in bai yi mata irin yadda ‘yan’uwansa suke yi mata ba, ya yi mata duk wani bayani amma bata yarda ba, shi ya sa ya yanke shawarar shiga wannan sana’a ta kaskanci ko shi ma ya samu kudi don ya kara kima a idon mahaifiyarsa, kuma ya huta da zagi da tozartawa a gaban kannensa ba iyaka!

Published in:  on April 27, 2008 at 2:56 pm Leave a Comment

A tsine!!!?

 Wani shugaban makaranta ne ya tambayi uban wani yaro me ya sa bai biya ku]in makaranta ba har yanzu? sai ya yi }arya ya ce: [anana bai kawo min takardar ba. sai ]an ya ce – da }arfi: “La ila Masalli ila A TSINE!!!”  sai duk kunya ta kama uban (Me ka\kika koya?)

 

Published in:  on April 21, 2008 at 9:10 pm Comments (1)

Nana Khadija Uwar Muminai

 

Assalamu alaikum. ‘Yan uwana yara  zan ba ku tarihin wata babbar mata cikin iyayen muminai.  Sunanta Khadijah bintu Khuwailid. Ita ce farkon matan Annabi (S A W) Ita ce farkon wadda ta fara muslinta, Ita ce kuma ta haifawa Manzon Allah (S A W) duka ‘ya yansa ban da Ibrahim. ‘Ya’yan nata su ne: 1) Abdallah, 2)Alqasim, 3) Zainab, 4) Rukayya, 5) Ummu kalsum, 6) Fadima. Yanzu ina so wani ko wata ta ba mu tarihin wata Sahabiyar a takaice kamar yadda ni ma na takaita.

Amina M. Muslim.

 

Published in:  on April 18, 2008 at 2:21 pm Leave a Comment

Bayan wata daya jal da bikinsu…?

 A cikin watansu na farko bayan bikinsu, ango na ganiyar angwancinsa, amarya na cin amarcinta da tsinke, suna modar madarar  soyayya, saboda shakuwa da kaunar dake tsakaninsu kamar sa cinye juna….. Kai abin dai ba’a cewa komai. Suna cikin wannan aljanna duniya sai KWATSAM ba sai mahaifin angon nan ya nemi ya saki matarsa ba! abu kamar almara, ashe wai da gaske yake! Angon  ya dauka wani mummunan laifi amaryar ta yi wa mahaifin nasa, ko mahaifiyarsa, ko wani daga cikin magabatnsu, ko kuma wata muguwar illa ce ta bayyana a gareshi game da ita… Uban ya ce duk ba daya, “Dalilin da ya sa na ce ka sake ta; saboda wanta da yake auren kanwarka tun shekaru da suka shude ya sako min ita don rashin mutunci; ni kuma  duk wanda ya yi min kan kara sai na yi masa na itace! Don haka kai ma ka sakar musu ‘yarsu” da yaron ya ji wannan ne 

 dalilin sai ya ce: baba da binciki aka yi aka ga me ya hada su, maimakon wannan mataki” uban sai ya kada baki ya ce: “Wato ’yan ubanci za ka nuna, da cikinku daya ai da ba sai na ce ka sake ta!” Dan ya ce wallahi ba haka ba ne… ya yi juyin duniyan nan da mahaifinsa, ya ce sam. Ya yi kuka kamar hawayensa ya kafe, amarya kuwa cutar yau daban ta gobe daban saboda zulumi, kullum sai su zauna su yi dan koke kokensu, su dan yi ‘yan shawarwari su tashi. Rannan  ya je ya samu baffaninsa ya gaya musu halin da ake ciki, suka tausaya matuka, suka je suka yi ta bai wa dan’uwan nan nasu baki, amma kamar turi, suka ce  masa to su dai wannan abu ya fi karfinsu. Ya kuma  tsurewa, amma  dai bai karaya ba, sai ya garzaya wurin wani aminin mahaifin da shi kadai yake iya sa shi ya yi abin da bai niyya ba, da ya yi masa bayani, sai ya ce tashi mu tafi ta kwana gidan sauki! 

Ango ya yi kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha don murna, har da zai yi wa amaryarsa waya  ya yi mata albishir, sai dai ya dakata ya ga yadda za ta kaya. Da ya je ya same shi, dan mutumin nan ya hada girar sama da ta kasa ya ce kwata-kwata ba za ta saku ba. Wato har da kai za’a hada baki a ci min mutunci?! Da dai ya ga ba sarki sai Allah, shi ma sai ya ce: “dana sai dai in taya ka da addu’a, amma abin ni ma ya fi karfina!” Angon  nan kamar ya barke da zawo, ya nufi gida a dimauce kamar ya yi hauka.

Daren nan kwanan zaune suka yi suna ta shawarwari, da asussuba sai ya ji bugun kofa ba-ji-ba-gani, yana budewa sai ya ga kannesa ne da suke ciki daya a firgice. Ya ce masa lafiya?! Sai ya ce: Umma jiya ba a gida ta kwana ba! Baba ya kore ta saboda wai tafiyar hawainiyar da kake yi wurin zartar da dokar da ya ba ka ta sakin wance

Ango ya ce: “Inna lillahi wa inna ilaihir

Raj’un” ya shiga gida, matar ta taso hankalinta a tashe ta

ce masoyina mai ya faru? Ya ce ba komai, bara in je

masallaci in dawo, yana salla amma hankalinsa ba yana

wani wuri, bayan ya gama zikrin safiya, sai ya kasa komawa

gida, sai ya nufi gidansu don ya tabbar menene

ha}i}anin abin da yake faruwa.

Da ya shiga falon uban sai ya tarar da shi fuskarsa a murtike

kamar an aiko masa da mutuwa, kafin ya ce masa

“Ina kwana” sai cewa ya yi wallahi in ba ka saki yarinyar

nan cikin gaggawa ba a bakin auren uwarka! kuma

yanzun nan ka je ka kawo min mukullin gidanka – da

yake dama uban ne ya gina masa– ango dai ya ga abin

ya fuce “min sharrin” ya kai “ma hala}a” sai ya tafi gida,

idonsa jawar saboda kuka, ya je ya samu amaryarsa, ya

kwashe labari baki ]aya ya gaya mata, don haka yanzu

dai ba wata mafita illa su dangana su rabu, su yi wa juna

addu’a alheri….. Haba take amaryar ta yanke jiki ta fa]i,

yana shafa mata ruwa yana yi mata fifita, yana ba ta

ha}uri, yana ce mata komai }addara ce ta Allah….!

Shi ma yana share nasa hawayen da hankiji. Suna

cikin wannan hali sai ga uban a kansu, ya ce rubuta

takardarta ka ba ta “mu kowa ya ci tuwo da mu miya

ya sha!” wasu da suke tare da uban suna ta ba shi

baki, amma kamar dutse suke yi wa magana, yaron

nan dai da ya ga ba sarki sai Allah, ya ]auki takarda

da biro, ya rubuta mata saki ]aya, suka rungume juna

a gaban mutane suna ta kuka, amma uban nan ko a

jikinsa, sai da ya ga ya ba ta takardar nan hannu-dahannu

sannan ya tafi ya kyale su.

Yanzu dai tuni har sun rabu! Kuma Allah ka]ai ya

san irin mawuyacin halin da kowannesu yake ciki!

FA[AKARWA GA IYAYE:

 

 

Sau tari irin wannan

 

 

Published in:  on April 17, 2008 at 11:00 am Leave a Comment

Allah ya kawo ranar da wance za ta je Unguwa!!!

 Ko shakka babu cewa agalabiyyar maza ba sa son matansu su rika yawan fita unguwa barkatai, kuma da ma wannan shi ne abin da shari’a ta yi umarni da shi; wato mata su zauna a gida (in ba wata lalura ba) amma shi wannan gogan namu kullum addu’arsa Allah ya kawo ranar da matarsa za ta tambayi unguwa, ya yi sauri ya bar ta idan ya ga ma ta jima ba ta tambayi unguwa ba, har tayi yakan yi mata ya ce: “wance ba ku da biki ko suna ne?” Ko kun san me yasa kullum mijin nan burinsa matar ta ce za ta je unguwa? Saboda ita a ka’idarta in kika ga ruwa ya taba jikinta to na sama ne, ko tsarki za ta yi, ko wankan tsarki, ko kuma alwala, in ba haka ba, in za ta shekara zancen wanka bai taso ba, ballantana a yi maganar ado da kwalliya, amma duk ranar da za ta tafi unguwa in ta caba ado sai ki dauka a ranar aka kawo ta dakin miji,  shi kuma yana so ya riga ganinta a cakare,  ba kullum kamar an  tono ta daga rami ba, yana ganin ta yana firgita!

A ganinki me yasa wannan mata ta zabi kullum ta rika zama busu-busu, in dai ba unguwa za ta ba, kuma wace shawara za ki bai wa irin wadannan kazaman  na ga-ni-kashe-ni

 

Published in:  on April 16, 2008 at 12:35 pm Leave a Comment

Gidan Qais ibn Asim Assa’dy (RA)

 Lokacin da  Qais ibn Asim Assa’dy (RA) -daya daga cikin Sahabbai– yake cutar ajali, ya tara  ‘ya’yansa  ya ce musu: “Ku yi  aiki da abin  da zan gaya muku; don ba wanda za ku yi aki da maganarsa da ya fi ni son ya gaya muku abin da zai amfane ku. Idan  na cika kada ku yi min kururwa; don na ji Annabi (SAW) yana hana a yi wa mamaci ihu,  kuma shi ma da ya rasu ba’a yi masa ihu ba, ku yi min likkafani da kayan da nake sallah da su, ku shugabantar da manyanku … ku nemi na-kanku, don ku wadatu daga mutane, ba ku ba maula; don maula ita ce hanya mafi kaskanci da mutum zai bi don samun na abinci…”  

 

Published in:  on at 12:33 pm Leave a Comment

Tambaya 0003

 

Tambaya:

Mace ce mijinta ya ba ta  maganin zubar da ciki ba ta sani ba,  kuma cikin nata ya zube. Don Allah malam: Menene hukuncin wannan miji, kuma menene hukuncin aurensa da wannan matar, kza’a iya cewa ya yi kisan kai,  wane  mataki ya kamata ta dauka, kuma menene hukuncin zubar da ciki a musulunci?

Maryam Usman

BISMILLAHIR     RAHMANIR         RAHIM

Alhamdulillah, Wassalatu Wassalamu ala Rasulillah, Wa ba’adu:

‘Ya’ya ni’ima ce daga Allah Subhanahu Wata’ala. Annabawa da bayin Allah na kwarai sun roki Allah da ya ba su’ ya’ya. Kashe yaya don jin tsoron talauci ko kunya, ko wahalar reno al’ada ce ta jahiliyya; sawa’un jahiliyyar zamanin yanzu ko ta da.In har kana son sanin girmar ni’imar da Allah ya yi maka ta ‘ya’ya, ka tambayi wanda ko wadda ba’a taba yi masa haihuwa ba.

Danganeda tambayoyinki kuma:

1. Ina hukuncin mijin da ya bai wa matarsa maganin zubar da ciki, sai ta sha ba tare da saninta ba, kuma cikin ya zube? Amsa: Zubar da ciki a kowane mataki yake; (watannin farko, tsakiya, ko karshe) – ba tare da wata larurar da shari’a ta yarda da ita ba – ya haramta a zance mafi inganci na malamai, sawa’un wanda ya yi sanadin zubar da cikin daya daga cikin iyayen dan ne ko waninsu.

2. Menene hukuncin aurensu? Amsa: Aurensu ya na nan daram.

3. Shin za’a dauka ya yi kisan kai? Amsa: Ya dogara bisa ga halin da aka zubar da cikin; idan cikin ya kai wata hudu ko sama da haka, to za’a iya cewa ya yi kisan kai, tun da yaro a wannan lokaci ya na da rai, kamar yadda ya zo a Hadisi na hudu na Arba’una Hadis.In kuma cikin bai kai wata hudu ba, to ya yi babban laifi, amma ba za a ce ya kashe rai ba, don kuwa a wannan hali yaro ba’a hura masa rai ba.

4. Wane mataki ya kamata ta dauka? Amsa: Ita dai ba ta yi laifi ba, tun da dai ta yi shi ne bisa rashin sani. kamata ya yi kuma ta yi wa mijinta nasiha da ya tsoraci Allah, ya yawaita istigfari da ayyuka na gari. Ita kuma nan gaba sai ta sa hankali, kar ta sha wani magani ba tare da shawarar likita ba. Allah ya kiyaye na gaba.

5. Menene hukuncin zubar da ciki a musulunci? Amsa: Hukuncin zubar da ciki a musulunci haramun ne; sawa’un sabon ciki ne, ko tsoho. Amma in akwai wata larurar da shari’a ta gamsu da ita, to ana iya zubar da ciki. Alal misali: Bakin likitoci ya zo daya akan cewa; in ba’a zubar da cikin nan ba, uwar tana iya rasa ranta, ko za ta jirkata, ko wani abu mai kama da haka, a irin wannan halin, ya zama dole a zubar da cikin don a ceci ran uwar. Wallahu A’alam.

Dr. Bashir ibn Imam Ali       

 

Published in:  on at 12:31 pm Leave a Comment

Kananan Hukumomi Albishirinku

 

A irin marka-markar da ofishin “A1 Nana” yake tsalawa a fagen tarbiyya, zamantakewar aure, da abubuwan da suka shafi mata, mamakon alheransa ya fara shatata a kananan hukumomin Jihar Kano (44) ta hanyar wani kwarya-kwaryar shiri da ofishin mai bai wa mai girma  gwamna shawara akan ayyuka na musamman (bangaren mata) ya shirya.  

A wata zantawa da Mujallar iyali ta yi da shugabar wannan ofis  Haj. Mariya Sanusi Mahdi game da manufofin wannan shiri, da kuma abin suka yanke shawarar hada-kai da ofishin “A1 nana” don gudanar da wannan aiki, sai ta ce: Babbar manufar wannan shiri agazawa iyaye mata wurin inganta rayuwarsu ta aure, da taimaka musu wurin tarbiyyar ’ya’yansu, da kuma sa su a hanya  wurin neman na-kansu.

 

Game da abin da ya sa suka zabi su yi taimakekeniya da “A1 nana cewa ta yi: Mun yanke wannan shawara ne saboda, wannan ofis-A1 nana- ya yi fuce da nagartattun tsare-tsare, kyawawan manfofi, hanyoyin zartarwa masu tasiri da ban sha’awa, da aiki tukuru, ga kuma matukar burin da yake da shi na tallafawa mata mazauna karkara, da dai wasu tsare-tsare masu kayatarwa. Kuma ya yi mun gani.

Shi kuwa shugaban ruko na ofishin “A1 nana” Eng. Bashir Adamu Aliyu nuna farin-cikinsa ya yi game da wannan goron gayyata, ya kuma yi alkawarin in sha Allahu kwalliya za ta biya kudin sabulu.

Da Mujallar iyali ta tuntube shi akan tanadin da ofishinsa ya yi gameda  wannan  shiri sai ya ce: Za mu fitar da cikakken bayani akan haka nan gaba,  amma dai za mu fi mayar da hankali ne akan: 

TARBIYYA: (Muhimmacinta fa’idojinta, hanyoyi, da dabarun yinta, kurakuren da suke aukuwa a cikinta, da hanyoyin magancesu 

ZAMANTAKEWA (Shawarwari ga iyaye danganeda auren `ya`yansu – zabi, nema, kayan aure da biki da tariya– Rayuwar iyali mafificiya -Hakkokin ma`aurata, zaman lafiya da taimakekeniya da sadaukarwa a rayuwar aure- Mace-macen aure-yawaitarsa, illolinsa, abubuwan da suke kawo shi da magungunansu)

SANA’O’I: koyar da wadannan sana’o’i (sabulun wanka, man shafawa, abincin jarirai, da maganin kwari). 

 

Published in:  on April 5, 2008 at 2:04 pm Leave a Comment

Ba duka ne kadai magani ba

wata rana wani malami mutumin Najeriya yana zaune a masallacin Annabi Tsira da aminci su tabbata agareshi, akusa dashi akwai wani Balarabe yana karatun Qurani, sai malamin ya hango wani yaro aguje yazo ya sunbanci Babansa yana farin ciki, amma mutuminnan yai kunnen uwar shegu da yaronnan ko daga kai baiyi ya kalleshi ba, bai kuma ce uffan ba . 

   Da yaron yaga haka sai ya juya ya tafi. can wajen sallar magriba sai ga yaronnan ya dawo yasake gaida Baban nasa kamar yadda al adarsu take wato ya sunbance shi

nan-da-nan  Babansa shi ma ya rungume shi ya zaunar da shi suka ci gaba da hira irin ta yaro da Babansa.

    Malamin nan yana kallon duk abinda yake faruwa, amma abinda ya dare masa kai shine yadda Uban yaron yaki ce masa : Bata dahu ba balle ta kone, a karon farko amma yanzu ya kula da shi sosai. Da aka jima sai Malamin nan ya matsa kusa da mutumin nan ya tambayeshi dalilin haka, sai Uban yaron yace:- Yaron ya san laifinsa bai je makaranta bane sai maza ya ruga yatafi da ya dawo kuwa muka shirya.

     To yaku Iyaye ashe akwai matakai da yawa na tarbiyya da zamu yiwa yayanmu kafin aje ga duka? 

kamar su;-

rashin kallo.

ishara da fuska.

kifta ido.

karamar harara.

Kin fita dashi unguwa.

Hana shi rabin kudin alawar da ake bashi zuwa makaranta, misali in Naira goma ne sai abashi Naira biyar.
      Daga Hamza Aliyu Ibrahim.

Published in:  on April 1, 2008 at 5:44 am Leave a Comment