Tambaya ta 0002

 Tambaya: Menene matsayin kaffarar wanda ya yi rantsuwa, da ya tashi kaffara ya yi azumi, ba tare da duba abubuwanda aka ce ya yi kafin azumi ba?                                 Maryam Husaini Falaki

***

Amsa: Kaffarar wanda ya yi rantsuwa kuma ya warware ta ita ce: ciyar da miskinai guda goma, ko ba su tufa, ko kuma ‘yanta bawa, kuma yana da zabi wurin gabatar da kowanne daga cikin abubuwa guda uku da aka ambata, idan kuma ya kasance ba shi da halin da zai yi daya daga cikinsu, sai ya yi azumin kwana uku.Saboda haka, danganeda wannan tamabayar, idan ya zamana ya yi azumin ne domin rashi, to kaffararsa ta yi; babu komai a kansa, amma idan ya kasanace ya yi azumin ne tare da cewa yana da halin da zai iya ciyar da miskinai, ko ba su tufa, kaffararsa ba ta inganta ba, ya wajaba a gareshi ya ciyar da miskinai goma, ko ya ba su tufa, domin abin da ya yi ya sabawa fadin Allah a cikin Alkur’ani (Suratul Ma’ida aya ta 89)

Allah shi ne mafi sani.

Dr. Muhd. Alhaji Abubakar
 

Published in:  on March 31, 2008 at 9:03 am Leave a Comment

Nana Khadija Uwar Muminai

 

Assalamu alaikum. ‘Yan uwana yara  zan ba ku tarihin wata babbar mata cikin iyayen muminai.  Sunanta Khadijah bintu Khuwailid. Ita ce farkon matan Annabi (S A W) Ita ce farkon wadda ta fara muslinta, Ita ce kuma ta haifawa Manzon Allah (S A W) duka ‘ya yansa ban da Ibrahim. ‘Ya’yan nata su ne: 1) Abdallah, 2)Alqasim, 3) Zainab, 4) Rukayya, 5) Ummu kalsum, 6) Fadima. Yanzu ina so wani ko wata ta ba mu tarihin wata Sahabiyar a takaice kamar yadda ni ma na takaita.

Amina Muhd. Muslim. 

Published in:  on at 9:00 am Leave a Comment