Gidan Annabi (SAW)

Anas dan Malik  (RA)  ya ce: Annabi (SAW) yana daga cikin mutanen da suka fi kowa kyawun hali, wata rana sai ya aike wata bukata, sai na ce WALLAHI BA ZA NI BA! Amma a raina ina da niyyar zuwa, sai na je na hadu da yara a kasuwa muka yi ta wasa, ban ankara ba sai na ji Annabi (SAW) ya danke ni ta keyya, da na waiwaya sai na ga yana dariya! Yana cewa “Kai dan Anas kama hanya ka tafi inda na aike ka” sai na ce masa to manzon Allah bara in tafi. Ya ce shekarata (10) ina yi masa aike aike bai taba ce min don me ka yi kaza, ko ba ka yi kaza ba (Muslim

Published in:  on March 26, 2008 at 10:57 am Leave a Comment