Abu Hurairah (RA) Duk lokacin da zai fita, ko ya dawo gida, sai ya je bakin kofar dakin mahaifiyarsa ya ce: “BABATA Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu. Sai ta ce: “Wa alaikumus Salam wa rahmatullahi wa barakatuhu DANA” Sai ya kuma cewa: “Allah Ya rahamshe ki; saboda tarbiyyar da kika yi min ina karami, ita kuma sai ta ce: “Kai ma Allah Ya rahamshe ka, ya saka maka da alheri, ya kuma yarda da kai; saboda biyayyar da kake min bayan ka girma” Daga cikin biyayyar da ya yi mata bayan ya girma: Akwai: 1- Rokon Annabi (SAW) da ya yi, kan ya yi mata addu’a ta musulunta, ya yi mata, kuma ta musuluntar. 2- Shi yake jigilar kai ta, da dakko ta daga ban daki; da yake makauniya ce. Bai je haji ba har ta rasu.