Ladubban yin Sulhu Tsakanin Masu Gaba

Gaba tsakanin musulmi babban zunubi ne; domin Allah ya wajabtawa musulmi son juna da kyautata wa juna, shi ya sa gusar da wannan zunubi ta hanyar yin sulhu tsakanin masu gaba ya zamo ibada ce da Allah yake so. Ga wasu ladaddakin wanda ya aikata wannan alheri.

1- Rabauta da rahamar Allah: Allah Ta’ala yana cewa a cikin ma’anar wata aya: ((Hakika muminai ‘yan uwan juna ne ; saboda haka ku sulhunta tsakanin ‘yan uwanku, ku kuma ji tsoron Allah domin ya rahamshe ku)) (Hujurat: 10).

2- Samun soyayyar Allah ; domin duk wanda ya kyautatawa ‘yan uwansa Allah yana son sa kamar yadda ya ce a ma’anar wata aya: ((Ku kyautata, domin kuwa Allah yana son masu kyautawa)). (Bakara: 195). Sulhu kuwa kyautatawa ne ga ‘yan uwa musulmi.

3- Samun ladan yaye wa musulmi matsala da gusar musu da wata cuta ; domin tabbas sabani tsakanin musulmi yana dauke da cutar da su duniya da lahira. Allah ya azarta mu da yi masa biyayya da kuma taimakon bayinsa.  

Rabi’atu Aliyu Umar (Umm A’isha).

Published in:  on February 9, 2008 at 11:25 am Leave a Comment

Habaka Son Allah da Manzonsa a Zukatan ‘ya’ya

Habaka son Allah da manzonsa a zukatan yara ba karamin mahimmanci ne da shi ba, don wannan zai sa su rika bin Allah da manzonsa sau-da-kafa, a komai wanda wannan ya hada da biyayya ga iyayensu. Wasu daga cikin hanyoyin dasa wa yara ko habaka kaunar Allah a zukatansu su ne:

1. Iyaye su rika nuna son Allah a mu’amalarsu

2. A rika yi wa yaro bayanin waye

3. Gaya wa yaro ni’imomin da Allah ya yi masa

4. Gayawa yaro cewa komai Allah ne yake bayarwa

5. Gaya yaro kyautar da Allah ya shirya wa mai yi masa biyayya

 Zainab Ibrahim

Published in:  on at 11:16 am Leave a Comment

Wa zai Canka!?

Mai kokari kawai nake so ya yi Magana.

Af! Assalamu alikum, shekarata takwas, kuma sunan matar Annabi ta farko ne da ni; Khadija, kuma a Madina aka haife ni, kai  Allah na gode maka!

Ga wasu sunaye guda hudu na wasu manyan mutane a musulunci:

1- Abubakar Saddik.

2- Ali bin Abi Talib.

3- Umar Bin Khattab.

4- Usman bin AffanTambayata a nan ita ce:

  •  Su wanene wadannan mutanen? Annabawa ne ko Sahabbai? Ko malaman makaranta?  
  • Menene taken kowanne? 
  • Na Jera wadannan sunayen gwargwadon harufansu na farko, ku kuma ku jera su gwargwadon daraja da kuma zamanin kowanne daga cikinsu. 
  • Hada kokarin bara da na bana ki nemo amsa. Ina jiran ki Wassalamu alaikum.

Kawarku Khadija Muhd. Muslim

Published in:  on at 1:29 am Comments (1)

Kwas na musamman don ‘yan mata

Bangaren matasa da ‘yan mata na wadannan cibiyoyi masu albarka (A1 families da Nana Asma’u Women Center), ya gabatar da kwas na matasa ‘yan mata (Teenage Program) na farko wanda a ka gudanar  daga ranar 30/12/2007 zuwa 01/01/2008.

snapshot03.jpeg  snapshot02.jpeg  snapshot07.jpeg

Manufofin wannan shiri

  • Samar da mata na gari masu imani da Allah da riko da koyarwar addininsu tare da wayewa ta zamani don gyaran al’umma.
  • Sanya ‘yammata a hanyar zama kwararru akan duk abubuwan da suka shafi mata a addininsu da rayuwarsu ta yau da kullum.
  • Dasa tushen samar da rayuwar iyali ingatacciya, ta buga misali.
  • Taimakawa iyaye wajen tarbiyyar ‘ya’yansu da gano irin abubuwan da suka dace da ‘ya’yan don karfafarsu a kai.
  • Gano da kokarin shawo kan matsalolin tarbiyya, alakar ‘ya’ya da iyayensu, da zamantakewar aure tun kafin su bayyana.
  • Samar da bincike da rubuce rubuce a kan hanyoyin tarbiyya da kura-kuran da ke afkuwa cikinta don magance matsalolin da su ke haifarwa a al’umma.

Abubuwan da shirin ya kunsa:

 Shirin ya kunshi laccoci da wasannin kwaikwayo (da harshen Larabci) da kacici-kacici (da harshen Hausa) da kuma mahawara (da harshen Turanci) baya ga horo na musamman a kan amfani da kwamfuta.

Shirin, wanda Mai bawa gwamna shawara a harkar mata, Hajiya Mariya Sanusi Mahadi ta bude, ya samu halartar ‘yan mata sama da 60 kuma dalibai na farko da wadannan cibiyoyi suka fara horaswa (trainers) ne suka gabatar da wannan kwas din gaba dayansa.  

Laccocin da aka gabatar, sun hada da:

  • Kissoshin Magabata Mata – Asma’u Bukhari Safwan,
  • Kula da kai (ko Tsaftar Jiki) – Binta Imam,
  • Lokacin balaga – Hassana Sani Darma,
  • Alaka da maza da Suturar ‘ya mace – Fatima Isma’il,
  • Abubuwa biyar kafin biyar – Hauwa Uba Sa’id
  • Abubuwan da Musulunci ke nema daga Matasa – Jameela Abdul Azeez
  • Jinin Haila da hukunce-hukuncensa – Sadiya Adamu Aliyu

Daga cikin muhimman abubuwan da shirin ya yi akwai jin ra’ayoyi, shawarwari da korafe-korafen yaran da suka shiga shirin da nufin samar da hanyoyin magance su.

Idan a ka ci gaba da bibiyar wannan fili za a samu karin bayani da kuma sakamakon wannan bincike da aka gudanar.

Da yardar Allah, nan gaba kadan, za mu gudanar da wani shiri na musamman don horas da iyayen wadannan yara da sauran iyaye game da hanyoyin tarbiyyar matasa da kuma sanar da su irin abubuwan da ‘ya’yansu ke korafi a kan su domin daukar matakan da su ka dace. 

A karshen wannan kwas din, an rarrabawa matasan kyaututtuka na littattafai, man shafawa, turare, man goge kaushi da sauransu.

Published in:  on at 1:25 am Leave a Comment

A Dinga Sara ana duban Bakin Gatari

‘Yar uwa! Kada ki manta da cewa duk mai rai fa zai mutu, kuma kowa zai shiga kabari, kabari kuwa dayan biyu ne, ko dai ya zama gidan ni’ima, gidan dadi da yalwa, kuma a fadadawa dan aljanna kabarinsa gwargwadon zira’i saba’in zai kasance cikin ni’ima har zuwa tashin alkiyama. Ko kuma ya kasance gidan azaba da kunci da wahala, za’a rika yi masa azaba tun daga kabarin ana kuma dukansa da guduma ta wuta. Kuma za’a kuntata masa kabarin a matse shi har kasusuwansa su rika kara, wanda da mutanen duniya za su ji da sun narke saboda tsananin firgita.Bayan kwanciyar kabari na iya shekarun da Allah ya kaddara, za’a tayar da mutane su tashi a firgice cikin dimuwa, kowa yana gudu ba tare da ya san inda ya nufa ba. Sannan a gurfanar da mutane a gaban Allah (SWT) wanda babu wani sarki a wannan ranar sai shi.Laa ilaha illallah! Hakika wannan rana ce ta tonon asiri, ranar tonon silili, ranar da babu abin da zai boyu sai an bayyana shi. Allah muna rokon ka ka kiyaye mu ka fitar da mu daga azaba, da tsoro da firgita na wannan rana, amin.‘Yar uwa bayan wannan hisabi, kowa za’a ba shi masaukinsa da ya dace da ayyukansa a mazauni na dauwama guda biyu; ko dai aljanna wadda fadinta ya kai nisan dake tsakanin sama da kasa. Ko kuma wuta mai tsananin zafi wadda har sashenta yana cinye sashe. Allah ka nisanta mu daga wuta, ka tserar da mu amin. Mai rabo shi zai shiga aljanna, Allah ka sa muna da rabo a cikinta da iyayenmu, da mazajenmu da ‘ya’ya da duk zuriyarmu, da duk musulmi baki daya. Marar rabo kuma wanda ya butulce wa ubangijinsa, ya bi son zuciyarsa, wannan wuta ce makomarsa. Allah (SWT) yana cewa:“Duk wanda ya kubuta daga wuta kuma aka shigar da shi aljanna hakika ya rabauta” (Ali Imran 85).Ya ke ‘yar uwa! Hakika bana shakkar cewa kina kaunar samun wannan babban rabo; don haka kada ki kuskura ki yaudari kanki, ko a yaudare ki, aljanna ta wadanda suka yi aikin kwarai ce, yin imani da ayyuka na kwarai su suke isar da mutum kofofin aljanna, kuma karantar Alkur’ani shi ne tsanin da ake hawa benayen aljanna.Saboda haka ‘yar uwa, ki nisanci duk wasu shaidanu da na ambata miki ire iren su a baya wadanda a ko yaushe suke son su ga kin yi wa Allah tawaye ki bata, kuma ki halaka. Ki toshe kunnuwanki daga duk wani kiran ‘yanci ko hudubar shaidan da za su rada miki, ki ce musu Ahir dinku.Ki zama baiwar Allah ta gari, mai tarbiyyantar da ‘ya’ya na gari wadanda za su zama manyan gobe. Ki zama babban jigo na gina wannan al’umma, kada ki zama hanyar ruguza ta.A karshe nake kara jaddada mana cewa yin riko da Alkur’ani da sunna shi ne zai kai mu ga gaci muddin mun rike su ba za mu bata ba, ba kuma za mu tozarta ba, a nan duniya, kuma a lahira mu samu sakamako mai girma. Allah ya sa mu dace Amin.Allah Ka nuna mana gaskiya kuma Ka bamu ikon bin ta, muyi aiki da ita,  Ka nuna mana karya Ka ba mu ikon guje mata. Allah Ka ba mu aljanna don rahamarKa, Ka nisantar da mu daga wuta. Allah Ka jikan iyayenmu da kakanninmu da ‘ya’yanmu da ‘yan uwanmu, da duk musulmi baki daya. Allah Ka yafe mana kura-kuran mu Amin. 

Safiyyah Hussain Falaki

Published in:  on at 1:19 am Leave a Comment

Wasiyyar Abil Walidil Baji ga ‘ya’yansa

Abu walid Albaji wani bijimin malami da ya rayu a karni na biyar ya yi wa ‘ya’yansa wata mahimmiyar wasiyya da ya kamata duk wani uba da malamin makaranta ya nazarinta, ya kuma amfana da ita wurin tarbiyyar ‘ya’yansa ko dalibansa.

Bara in dan tsakurowa mai karatu wani abu daga cikin wannan hamshakiyar wasiyya. 

  1. Ku kiyaye dokokin Allah a fili da boye.
  2. Ku kiyayi gina wani hukunci akan ilimin taurari, ko bokanci, domin wannan fitar da wanda ya gasgata shi yake yi daga addni, ya kuma shigar da shi cikin kangararru 
  3. Ba ku ba zulunci,  girman- kai,  hassada, gulma da munafunci 
  4.  Ku guji sauraron kade-kade; fitina yake haifarwa a zuci, da tunanin aikata sabo 
  5.  Kada dayanku ya fifita wani abin duniya akan danuwansa, sai ya rika yiwa danuwan nasa rowa saboda shi, ko ya juya masa baya, ko ya rika gasa da shi a ciki. Wanda Allah ya yi wa arzuki a cikinku to su ci tare da danuwansa, kar ya kadaita da shi, ya yi kokarin habaka dukiyar danuwansa, kamar yadda zai yi kokarin habaka tasa… ‘Yaruwa salon wasiyya salo ne na Annabawa da nagartattun bayi  a tarbiyya, kuma tasirinsa ya wuce duk yadda kike tsammani,  gwada shi ki ga bambanci. Allah ya sa mu dace  

 Batulu Aminu Dantata 

Published in:  on at 1:04 am Leave a Comment

“Tufka da Warwara”

An karbo Hadisi daga Abu Huraira Allah ya kara yarda da shi ya ce:        

An tambayi manzon Allah (S.A.W) cewa:  Ya Rasulallah! hakika (wance) tana sallar dare, ta yi azumin nafila da rana, tana aikata ayyukan alkhairi, kuma tana sadaka, amma tana cutar da Makotanta (da harshenta)! Sai ya ce: “Babu alkhairi a gareta tana daga cikin ‘yan wuta” sannan aka ce (wance) kuma tana salloli wajibabbu, ta yi sadaka da dan abu kadan, amma bata cutar da kowa. Sai Annabi (S.A.W) ya ce: “Ita yar aljanna ce”. (Bukhari fil adabil mufrad).

‘YAR UWA IDAN KIKA DUBA WANNAN HADISI ZA KI GA CEWA DUK ALKHAIRIN DA KIKA KULLA TO CUTAR KISHIYA YA WARWARE SHI. WANNAN SHI NE TUFKA DA WARWARA. ALLAH YA YA KIYAYE AMIN.

Ummu Huwailat

Jamilat Bint Abdul’Aziz Alkazauriyya. 

Published in:  on at 12:16 am Leave a Comment

Hankoron jijjige matsala Ya kai ga karyar Cutar jijjiga!

Wasu matan suna da ragon azanci wurin magance masalar da suka samu kansu a ciki, sai su yi gudun gara su tarar da zago, ko su debo ruwan dafa kansu, ko su janyowa kansa abin fada har abada ana ganinsu da abin.  

Haka ce ta sa na yi tunanin fadakar da ‘yanuwana bisa wannan susanci da wasu mata kan fada ciki.  A wani lokaci ‘yan shekarun baya, a asibitin Murtala na Kano, bangaren ‘yan haihuwa, dakin ‘yan jijjiga, wani labara ya faru abin takaici, abin haushi, kuma abin dariya duk a lokaci guda. Wata rana ce wani mutum ya zo da matarsa a asibiti a demauce ita da   ‘yanuwanta kamar a sussume, suka ce jijjiga take yi.        

Ganin cewa matar kwana guda kenan da haihuwarta, sai ga unguwar zomar (mid wife) ta karbe ta ta kwantar da ita da nufin ta auna ta don ta tanadi bayanin da likita zai bukata game da ita Da unguwar zoman ta dauko abin awon jini wato (Blood pressure) to ba sai ta ga mata ta runtse idanunta ba, amma kuma tana ta karkada kafadunta da hannayenta ita wai ba ta yarda ba jijjiga take yi!Da unguwar zoman ta fahimci dawan garin,  sai ta ce: “duk wadanda suka kawo ta su kauce su ba da wuri” Sai suka kama gardama suna cewa: ai in sun bar ta ita kadai za ta fado. Duk sun gama gigicewa.Ita kuma ta tsaya kai da fata sai sun ba su wuri. Da kyar dai suka hakura suka fita.

Bayan sun ba su wuri sai ta ce da ita: “Haihuwa!!!” dan daure ki bar min wannan hannun don na auna ki amma kina iya girgiza waccan!

Abinki da rashin sani, gaular taki sai kawai ta bi umarnin; Ta canza hannun da take girgizawa! Wai ita za’a auna ta, sannan kuma ko karaya ta yi, sai ta dan bude idonta kadan don ta fahimci me ake son ayi mata. 

Da unguwar zoman ta fahimci haka, sai ta kirawo mijin wanda yake cikin mummunan tashin hankali ta tambaye shi, ko waani abu ya faru a tsakaninsu?

Da yake baya son fadan sirrinsa. Sai ya ce ai malama kin san ita rayuwa ba’a  rabuwa da ‘yan matsaloli!  

To a nan ta fede masa biri har wutsiya, ta ba shi tabbacin cewa matarsa lafiyarta lau, cutarta ta matsaloli ce ba ta rashin lafiya ba! sai dai da hadin kansa za’a bar ta a asibiti ta yini, ta nutsu, sannan a sallame ta. Ita kuma matar daga bisani aka ja hankalinta cewa nan gaba ba haka ake nuna fushi ba, ta yi kokarin warware matsalar tare da mijinta a gida ba sai ta yi abin da za’a kawo ta asibiti ba don hadarin da zai iya shigar da ita.Allah ya kyauta.

Sadiya Adamu Aliyu       

Published in:  on at 12:05 am Leave a Comment

Da’awa cikin Dabara

‘Yanwana Mata Assalamu alaikum wa rahmatullah.

Bayan haka:

Duk inda musulma take ya kamata ta zama mai afani, mai kokarin isar da sakon Allah a duk inda ta samu kanta, musamman ga makusantata, iyalinta, kawaye, makota, da sauran jama’a.

Akwai hanyoyi da dama na isar da wadannan sakwanni, daya daga ciki ita karkata akalar zance zuwa wani abu da zai amfani masu sauraro.

Yawanci hirar farko da ake bude fage da ita a wurin tarurrukanmu na mata – kamar suna, biki, tariya dss- ita ce take wawashe yawancin lokacin zaman.

Alal misali in hirar wani fim aka fara, sai ki ga ita za’a yi ta yi har zuwa wani lokaci mai tsaho kafin a canza.

Haka nan in hirar “yau” ake; tsadar kayayyaki da shauransu, ko hirar wani anko da ya fito. dss.

‘Yar uwata yi amfani da wannan damar wurin bude fage da abin da zai amfani mutane don ki isar musu da sakon da kike so, amma fa ki yi la’akari da irin mutanen, da kuma irin taron.

Misali: bayan an gaggama gaisawa an huta, sai ki fara jan ta kusa dake da hira…

· “Ke kuwa a ganinki me ya sa yanzu cikin shege yake yawa tsakanin ‘yan mata”?

· “ke kuwa  wace mace ta fi burge ki a duniya”…. Me ya sa…?

·“A ganinki me ya sa yawancin ‘yan wuta mate ne?”

·    “Wa ya ji labarin da aka fada jiya a taskar labarai wata mata ta yi kokarin kashe mijinta…?” me ya sa ku a ganinku irin wannan take faruwa yanzu a cikin al’ummarumu, bayan da ko kusa ko alama ba bu su?”

· “Me ya sa zuwa gurin bokaye da ‘yan duba yake kara yawa ne musamman tsakanin mata?”

·  “Wa yake da masaniya game da kare hakkin kananan yara da ake ta yamadidi akansa?”

·“Ya mace za ta iya sa mijinta ya rika zama a gida?”

Da shauransu

Nan da nan sai ki ga hankalin mutane ya karkata kan abin da kika kawo, ke kuma ta hanyar hira, sai ki shigar musu da sakon da kike son shigarwa.

In kuma abin da kika kawo na tattaunawar bai ba su sha’awa ba, sai ki canza wani.

Fatima MK Yunus (Ummu Ibn Taimiyyah) 

Published in:  on February 8, 2008 at 11:38 pm Leave a Comment

SUTURA MUTUNCI

Assalamu Alaikum Wa rahmatullahi Wa barakatuh

Bayan haka, ya yar’uwata madaukakiya, ina fatan kina lafiya. Wannan wata  tsaraba ce nake dauke da ita, domin dai fatan mu shi ne mu gudu tare mu tsira tare.

Bayanin da na ke dauke da shi kuwa shi ne: akan HIJABI irin wanda shari’a ta yarda mu yi amfani da shi. Ya ‘yar’uwata! ki tuna fa gargadin da Allahu (S.W.T) ya yi mana dangane da sanya HIJABI irin na musulunci, inda yake cewa a cikin Suratul-Ahzab aya ta (59) (يَا أَيُّهَا النَّبِيُّ قُلْ لِأَزْوَاجِكَ وَبَنَاتِكَ وَنِسَاءِ الْمُؤْمِنِينَ يُدْنِينَ عَلَيْهِنَّ مِنْ جَلَابِيبِهِنَّ ذَلِكَ أَدْنَى أَنْ يُعْرَفْنَ فَلَا يُؤْذَيْنَ وَكَانَ اللَّهُ غَفُورًا رَحِيمًا) (59)Ma’ana: “Ya kai  wannan Annabi! Ka fadawa matanka da ‘ya’yanka da matan muminai, su kusantar da kasa daga manyan tufafinsu wannan zai fi sa a gane su, kuma kada a cutartar da su, Allah ya kasance mai yawan gafara, mai yawan jin-kai.” Da kuma fadin Allah (S.W.T) cikin Suratun-Nur aya ta (31) وَلْيَضْرِبْنَ بِخُمُرِهِنَّ عَلَى جُيُوبِهِنَّMa’ana:  “kuma su rufa mayafansu akan rigunansu.”Don haka ya ‘yar’uwata, jikanyar Nana Aisha! ki tuna fa lokacin da wannan aya ta sauka, matan sahabbai barguna suka  rinka lullubawa suna fita da su, don tsananin son Allah da Manzonsa, da kuma kokarin kiyaye dokokinsa.Kuma kina da masaniya akan cewar wadannan mata sun fi mu kyau da daraja da matsayi? Don su ne fa su Nana Aisha su Nana Zainab,  su Nana Ummu-salama, su Nana Fadima ‘yar fiyayyen halitta, da sauran matan sahabbai, (Allah ya yarda da su gaba daya). To, mu yau wane matsayi muke da shi? kuma wane kyau muke da shi? Da har za su hana mu bin dokar Allah (S.W.T)? don haka ne nake ganin ya kamata mu yi wa kanmu fada, mu kuma sake tunani, domin gyara wannan matsala mai matukar muhimmanci mu kuma nusar da ‘ya’yanmu da kannenmu akan suturar musulunci. ‘Yar’uwata! A nan ba ana nufin sai kin sayi yadi baki ko fari ko wata kala ta musamman kin dinka HIJABI  irin wanda ake kira HIJABI a yanzu ba, a’a ko wace irin sutura kika lullube jikinki da ita, zai iya zama hijabi, matukar dai ya cika sharuddan da musulunci ya gindaya. Ga su  kamar haka:-

1.  ya  kasance ya rufe miki jiki gaba daya.

2.  Ya kasance sakarsa tana da kauri, ba shara-shara ba.

3. Kada ya zama matsattse,ta yadda za’a iya ganin tudun abin da ya ke kasansa.

4. Kada ya zama tufafin alfarma ne.

5. Kada ya zama mai ado ko mai daukar hankali.

6. Kada ya yi kama da tufar maza.

7. Kada ya yi kama da tufar kafirai; domin duk wanda ya yi kamanceceniya da wasu mutane, to, shi ma yana cikin su.

Kuma ya kamata mu kiyaye cewar:- hijabi ba wai ya shafi matan Aure ba ne kawai, a’a ya shafi duk wata mace da ta balaga, ma’ana yadda sallah ta wajaba akan ki, to haka hijabi ma ya wajaba akan ki.. Daga karshe ina mai fatan Allah (S.W.T) ya ba mu dacewa, ya sanya mu fi karfin zuciyarmu, ya kuma sanya mu cikin masu fifita tsarin Allah akan son zuciyarmu. Amin

                                                                                  Daga:-‘Yar uwarki: ASMA’U BUKHARI SAFWAN

Published in:  on at 4:03 am Leave a Comment