Assalamu Alaikum Warahmatullah
‘Yar uwa a musulunci, hakika Addu’a tana da tasiri a rayuwarmu, musamman mata.
Yar uwata, Addu’a fa karki manta ita kanta ibada ce domin Allah (S.W.T) yace: “ku roke Ni zan amsa muku” suratu gafir.
Don haka duk abin ya same ki ‘yar uwa gaya wa Allah. sai ki sami maganin matsalar ki.
Sannan Annabi (S.A.W) ya ce: (Addu’a makamin mumini ce) kin ga ashe ba ki da wani abin kamawa wanda ya wuce Addu’a.Allah ya sa mu dace Amin.
Asma’u Bukhari Safwan