Don kar Mage ta Cinye!

Shehu Jaha ya saba kullum ya sayo gari, ganyaye (na ci) da kuma kayan marmari ya kawo gida, ita kuma matarsa ta saba ta dafa ganyayen, kayan marmarin kuma ta aika wa kwarta kyauta!

Kullum dare idan Jaha ya hakimci don ya kwashi girki da kayan marmari, ba abin da matar nan take kawo masa sai gurasa tsura!

Abin dai yana ta daurewa Jaha kai.

Rannan dai sai ya yi ta maza; ya tsaga bullensa ya tambayi matar:

“Wai ni ina ganyaye da kayan marmarin da nake shigowa da su kullum; ina kike kai su?” Sai matar ta kada baki ta ce:

“Abin da ka samu ka godewa Allah wannan shi ne rabonka!!! duk lokacin da na dafa wani abu MAGE take cinyewa”

Jaha ya dan tsaya tsai yana tunani akan maganarta, sannan sai ya yi wuf ya zabura ya dauke GATARINSA da yake rataye a jikin garu ya wurga shi  cikin akwati ya garkame.  

Sai matar ta tambaye shi:

“Jaha lafiya menene na buye gatari kuma?”

Sai ya ce:

“Na boye shi ne don kada mage ta gani ta cinye!

Sai matar  ta cika da mamaki, har ta yi wata irin shewa ta ce:

“Mahaukaci ne kai! Mage tana cin gatari ne!!

Sai Jaha ya ce mata:“Wallahi da hankalina sarai, amma ke me kike gani; yanzu magen da za ta rika cinye girkin dirhami goma, da kayan marmari na dirhami goman (ashirin kenan), INA GA GATARIN DIRHAMI UKU!!?”

Published in:  on February 16, 2008 at 5:36 am Leave a Comment

The URI to TrackBack this entry is: http://iyalina.wordpress.com/2008/02/16/don-kar-mage-ta-cinye/trackback/

RSS feed for comments on this post.

Leave a Comment