“Ko Uwaka Za ka yi”!?

Wata rana wani baywan Allah zai shiga ban-daki, sai wani dan karamin dansa ya tambaye shi:

“BABA ME ZA KA YI?”

Sai ya yi masa banza, to kin san yara da tambaya, sai ya kara tambayarsa

“BABA ME ZA KA YI?” 

Ya kuma yin shakulatin bangaro da shi, kamar dutse yake yi wa Magana.

Yaron nan dai bai hakura ba sai ya kara tambayarsa. “Baba me za ka yi”

Sai uban ya ka da baki ya ce: “UWAKA ZAN YI!” 

shike nan Magana ta fuce kamar yaro ya manta, wata rana babansa ya yi baki, ta kuma kamawa zai shiga ban-daki, sai yaron nan ya kuma yi masa irin waccen tambaya; “BABA ME ZA KA YI?” shi kuma uban sai ya yi masa banza, shi kuwa yaron sai ya kada baki ya ce: “KO UWAKA ZA KA YI?!”

Sai duk kunya ta kama mahaifin nasa a cikin jama’a.

DON HAKA a tarbiyya yana da kyau duk irin tambayar da yaro ya yi a ba shi amsa, kuma lallai ne a ba shi amsa ta gaskiya, kar a yi masa karya, kamar yadda wasu suke yi in yara sun  tambaye su, ko dai su hana su tambayar, ko su yi musu shiru, ko ma su gilla musu karya, sai bayan sun girma su yi ta kallonsu da abin.

Kamar idan sun ce musu ina kakarsu da ta mutu? sai a ce ta tafi unguwa za ta dawo!

Ko ta ina ake haihuwa? Sai a ce masa ta baki! dss 

Published in:  on February 11, 2008 at 8:45 pm Leave a Comment

KISHI

  • KISHI gishirin soyayya idan ya yi yawa ya baci; a dinga cizawa ana busawa.
  • KISHI kumallon mata idan ya taso miki ‘yar uwa ci gauta, ko lemon tsami, ko goro, ma’ana a nan ita ce  ki dinga HAKURI; in mutum ya yi hakuri sai ya dafa dutse ya sha romonsa, hakika Allah yana tare da masu hakuri.

                                                                 Gambo Shehu

Published in:  on at 8:32 pm Leave a Comment