Wani bawan Allah daga cikin nagartattun bayin da suka shude ya saki matarsa, kafin ta gama idda sai wasu suka zo takanas suka tambaye shi Me ya hada ku da wance ne har ka sake ta?
Sai ya ce: “
Mai hankali ba ya tona asirin matarsa”
Bayan ta gama iddar-ke nan ta fita daga hannunsa- sai suka kuma yi masa waccan tambayar dai, sai ya ce:
“Me ya hada ni da matar wani!”
Me ake koya a wannan kissa?