Da’awa cikin Dabara

‘Yanwana Mata Assalamu alaikum wa rahmatullah.

Bayan haka:

Duk inda musulma take ya kamata ta zama mai afani, mai kokarin isar da sakon Allah a duk inda ta samu kanta, musamman ga makusantata, iyalinta, kawaye, makota, da sauran jama’a.

Akwai hanyoyi da dama na isar da wadannan sakwanni, daya daga ciki ita karkata akalar zance zuwa wani abu da zai amfani masu sauraro.

Yawanci hirar farko da ake bude fage da ita a wurin tarurrukanmu na mata – kamar suna, biki, tariya dss- ita ce take wawashe yawancin lokacin zaman.

Alal misali in hirar wani fim aka fara, sai ki ga ita za’a yi ta yi har zuwa wani lokaci mai tsaho kafin a canza.

Haka nan in hirar “yau” ake; tsadar kayayyaki da shauransu, ko hirar wani anko da ya fito. dss.

‘Yar uwata yi amfani da wannan damar wurin bude fage da abin da zai amfani mutane don ki isar musu da sakon da kike so, amma fa ki yi la’akari da irin mutanen, da kuma irin taron.

Misali: bayan an gaggama gaisawa an huta, sai ki fara jan ta kusa dake da hira…

· “Ke kuwa a ganinki me ya sa yanzu cikin shege yake yawa tsakanin ‘yan mata”?

· “ke kuwa  wace mace ta fi burge ki a duniya”…. Me ya sa…?

·“A ganinki me ya sa yawancin ‘yan wuta mate ne?”

·    “Wa ya ji labarin da aka fada jiya a taskar labarai wata mata ta yi kokarin kashe mijinta…?” me ya sa ku a ganinku irin wannan take faruwa yanzu a cikin al’ummarumu, bayan da ko kusa ko alama ba bu su?”

· “Me ya sa zuwa gurin bokaye da ‘yan duba yake kara yawa ne musamman tsakanin mata?”

·  “Wa yake da masaniya game da kare hakkin kananan yara da ake ta yamadidi akansa?”

·“Ya mace za ta iya sa mijinta ya rika zama a gida?”

Da shauransu

Nan da nan sai ki ga hankalin mutane ya karkata kan abin da kika kawo, ke kuma ta hanyar hira, sai ki shigar musu da sakon da kike son shigarwa.

In kuma abin da kika kawo na tattaunawar bai ba su sha’awa ba, sai ki canza wani.

Fatima MK Yunus (Ummu Ibn Taimiyyah) 

Published in:  on February 8, 2008 at 11:38 pm Leave a Comment

SUTURA MUTUNCI

Assalamu Alaikum Wa rahmatullahi Wa barakatuh

Bayan haka, ya yar’uwata madaukakiya, ina fatan kina lafiya. Wannan wata  tsaraba ce nake dauke da ita, domin dai fatan mu shi ne mu gudu tare mu tsira tare.

Bayanin da na ke dauke da shi kuwa shi ne: akan HIJABI irin wanda shari’a ta yarda mu yi amfani da shi. Ya ‘yar’uwata! ki tuna fa gargadin da Allahu (S.W.T) ya yi mana dangane da sanya HIJABI irin na musulunci, inda yake cewa a cikin Suratul-Ahzab aya ta (59) (يَا أَيُّهَا النَّبِيُّ قُلْ لِأَزْوَاجِكَ وَبَنَاتِكَ وَنِسَاءِ الْمُؤْمِنِينَ يُدْنِينَ عَلَيْهِنَّ مِنْ جَلَابِيبِهِنَّ ذَلِكَ أَدْنَى أَنْ يُعْرَفْنَ فَلَا يُؤْذَيْنَ وَكَانَ اللَّهُ غَفُورًا رَحِيمًا) (59)Ma’ana: “Ya kai  wannan Annabi! Ka fadawa matanka da ‘ya’yanka da matan muminai, su kusantar da kasa daga manyan tufafinsu wannan zai fi sa a gane su, kuma kada a cutartar da su, Allah ya kasance mai yawan gafara, mai yawan jin-kai.” Da kuma fadin Allah (S.W.T) cikin Suratun-Nur aya ta (31) وَلْيَضْرِبْنَ بِخُمُرِهِنَّ عَلَى جُيُوبِهِنَّMa’ana:  “kuma su rufa mayafansu akan rigunansu.”Don haka ya ‘yar’uwata, jikanyar Nana Aisha! ki tuna fa lokacin da wannan aya ta sauka, matan sahabbai barguna suka  rinka lullubawa suna fita da su, don tsananin son Allah da Manzonsa, da kuma kokarin kiyaye dokokinsa.Kuma kina da masaniya akan cewar wadannan mata sun fi mu kyau da daraja da matsayi? Don su ne fa su Nana Aisha su Nana Zainab,  su Nana Ummu-salama, su Nana Fadima ‘yar fiyayyen halitta, da sauran matan sahabbai, (Allah ya yarda da su gaba daya). To, mu yau wane matsayi muke da shi? kuma wane kyau muke da shi? Da har za su hana mu bin dokar Allah (S.W.T)? don haka ne nake ganin ya kamata mu yi wa kanmu fada, mu kuma sake tunani, domin gyara wannan matsala mai matukar muhimmanci mu kuma nusar da ‘ya’yanmu da kannenmu akan suturar musulunci. ‘Yar’uwata! A nan ba ana nufin sai kin sayi yadi baki ko fari ko wata kala ta musamman kin dinka HIJABI  irin wanda ake kira HIJABI a yanzu ba, a’a ko wace irin sutura kika lullube jikinki da ita, zai iya zama hijabi, matukar dai ya cika sharuddan da musulunci ya gindaya. Ga su  kamar haka:-

1.  ya  kasance ya rufe miki jiki gaba daya.

2.  Ya kasance sakarsa tana da kauri, ba shara-shara ba.

3. Kada ya zama matsattse,ta yadda za’a iya ganin tudun abin da ya ke kasansa.

4. Kada ya zama tufafin alfarma ne.

5. Kada ya zama mai ado ko mai daukar hankali.

6. Kada ya yi kama da tufar maza.

7. Kada ya yi kama da tufar kafirai; domin duk wanda ya yi kamanceceniya da wasu mutane, to, shi ma yana cikin su.

Kuma ya kamata mu kiyaye cewar:- hijabi ba wai ya shafi matan Aure ba ne kawai, a’a ya shafi duk wata mace da ta balaga, ma’ana yadda sallah ta wajaba akan ki, to haka hijabi ma ya wajaba akan ki.. Daga karshe ina mai fatan Allah (S.W.T) ya ba mu dacewa, ya sanya mu fi karfin zuciyarmu, ya kuma sanya mu cikin masu fifita tsarin Allah akan son zuciyarmu. Amin

                                                                                  Daga:-‘Yar uwarki: ASMA’U BUKHARI SAFWAN

Published in:  on at 4:03 am Leave a Comment

Riga kafi ya fi Magani

Published in:  on at 3:49 am Leave a Comment

Imamu Shafi’i lokacin yana dan Yaro

Assalmu alaikum abokaina na Najeriya da na Madina,

Kun kuwa san yadda imamush shafi’a yake lokacin yana dan yaro?

To zan gaya muku, amma kafin nan barain fara gaya muku wanene shi ma tukuna IMAM ASSHAFI’I, sunansa (MUHAMMAD BIN IDRIS) Wani babban malami ne da aka Haifa a garin “Gazza”, wanda yake a Kasar “Palastine” -inda a yau yahudawa kullum suke kashe musulmi- a shekara ta (150) bayan hijira, ko da yake iyayensa mutanen Makka ne, kuma ‘yan Kabilar Kuraishawa ne, Kabilar Manzon Allah (s.a.w).

Ya nemi ilimi a wurin malamai masu yawa, a garuruwa daban – daban, musamman Makka da Madina. Daga cikin manyan malamansa da akwai Imamuna Maliku.Iliminsa ya kai ya kawo, ya tumbatsa har ya kafa mazahaba wadda ta zama daya daga cikin manyan mazahabobin Ahlussunnah wal jama’a guda hudu. Ya kuma rubuta littattafai masu yawa. Ga shi da yawan ibada, kullum sai ya yi sallar dare, ga shi da tawalu’u matuka da gaske, ba ya ganin kansa komai! Har Allah ya dauki ransa a shekara ta (204) bayan hijirar Manzon Allah (s.a.w).

Allah ya jikansa ya amfane mu da ilimummukansa.

Imamu shafi’i tun yana dan yaro an ce himma ce da shi kamar me, ga basira da hazaka, ga ladabi da biyayya, duk inda aka aike shi nan da nan zai yi sauri ya dawo, Babarsa tana son sa sosai saboda kirkinsa da kokarinsa. Ni dai Imamush Shafi’i yana burge ni, in sha Allahu sai na zama irinsa, na san kuma kuna so, to sai mu dage, kuma muce baban ninmu su rika yi mana addu’a.

Abdallah Muhd. Muslim (shekara 12).

Published in:  on at 3:39 am Leave a Comment

Soyayya a Ma’aunin Shari’a

Gabatarwa:

Ma’anar So:  So ga bil adama shi ne karkatar zuciya da juyawarda izuwa wanda ake so, sakamakon wani abu da ya janyo karkatar zuciyar kamar kyon halitta, ko na dabi’u da halaye,  ilimi da kwarewa a wani abu dss. Zuwa wanda take, ko yake so. Irin wannan so shi ake kira so mai dalili (Conditional love)Irin wannan so yana karuwa, kuma yana raguwa, sakamakon cancanzawar sababan da suke gudanar da shi.

Akwai so da ake ce masa marar sababi (Unconditional love) Wannan irin so wasu suna ganin karya ne, wasu kuma suka ce cuta ne; shaidan ne yake sanya shi da izinin Allah a cikin zukatan da suka gafala, suka bar gurbin da shaidan zai cike shi da irin wannan nau’i na “so” zan ci gaba da wannan kasida nan gaba.ws

Fatima Isma’il Ibrahim

Published in:  on at 2:35 am Leave a Comment