Mahimmancin Lokaci a Rayuwar Matashiya

 Da sunan Allah mai tarin rahama da yawan  jinkai. Tsira da aminci su tabbata ga mafi daukakar annabawa da manzanni; Annabi Muhammadu (SAW)       

Bayan haka zan yi amfani da wannan kofa domin jan hankalin ‘yan uwana ‘yan mata matasa game mahimmancin lokaci, da kiyaye shi. Ya ‘yar uwa hakika yana da matukar kyau ki san kimar lokacin da Allah (swt) ya tanadar gareki, haka nan  ki san yadda za ki yi tattalinsa; domin ki amfani kanki da al’ummarki da shi ki nemi guzirin tafiya lahira, kar ki zauna ki shantake kina sharholiya, da karance-karance marasa amfani, ko kallon fina-finai,  ko hotuna masu nuna tsiraici, ko tunane-tunane marasa kan-gado, ko maganganu wadanda ba su kamata ba. Wadannan duk ba za su amfane ki da komai ba, sai dai su kara dilmiyar dake a cikin halaka, da jawo miki da-na-sani.

Ki tuna lokaci ba ya jiran kowa.!Yi kokari ki ga kin amfana da lokacin da kike da shi, ki kasance a koda- yaushe cikin

·        Ambaton Allah, da

·        Yin kowace sallah akan lokaci,

·        Yawaita yin Nafilfili,

·        Yawaita karatun Alqur’ani

·        Karanta littatattafai na ilimi da zaki karu,

·        Sauranron kasa-kasai na wa’azi ko lacca wadanda za ki amafana da su duniya da lahira, ·        Yin zikirin safiya da maraice wadanda ake kira (Alma’athurat) da makamantansu.

·        Taya mahaifanki aiki a gida kamar girki, shara, yi wa kanne wanka dssMatukar kin kiyaye wadannan abubuwa, da shauran ayyuka na alheri da ban zayyana ba, ina mai yi miki albishir da in sha Allah za ki kasance cikin rayuwa ta jin dadi da samun biyan bukata, da samun kusanci da Allah (swt) tare da samun yardarsa, da samun karin kaunar iyaye da yardarsu, kuma ki rika jin cewa kina da amfani a wannan rayuwa, ba ‘yar rakiyar zuwa duniya b ace. Don haka sai ki kiyaye, ki guji zaman bata lokaci, ki zauna kurum ba tare da kin yi amfani kanki da wani abu ba; domin wannan shi zai kara jawo miki abin da zai cutar dake, da jawo miki wasu-wasi, da bacin rai da shakka. Saboda haka, nake gargadin ‘yan uwana matasa da su dage da yin addu’a kowane halin da suka sami kansu da su yawaita karanta wannan addu’a: “ALLAHUMMA INNI A’UZU BIKA MINAL HAMMI WAL HAZANI WA A’UZU BIKA MINAL AJZI WAL KASALI, WA’A UZU BIKA MINAL JUBNI WAL BUKHLI,  WA A’UZU BIKA MIN GALABATIDDAINI WA QAHRIRRIJALI” Idan har kina yawaita karanta wannan addu’a da bibiyar ma’anarta, insha’Allahu,  Allah (s.w.t) zai ya ye miki damuwarki, da bakin ciki, ko bacin rai.

Ya ‘yar uwa ta! Ya kamata a kowane lokaci ki kasance cikin shiri da tanadi domin wannan rana mai zuwa (Alkiyama). Kuma kada ki damu da wani abu na rayuwar duniya wanda ba tabbatacce ba, har ranki ya rinka baci akansa don baki same shi ba kiyi hakuri, hakika Allah yana tare da masu hakuri, kuma lallai babu wani tabbataccen abu sai aikin mutum na kwarai.Allah (s.w.t) yana cewa:  “wanda ya yi aiki na gari daga cikinku, namiji ko mace zamu raya shi rayuwa mai dadi, kuma zamu saka musu da mafi kyon abin da suka aikata”(Suratun-nahli)Allah yasa mu dace Amin

                                                                                                 MARYAM JAMILA MUHAMMAD 

Published in: on February 7, 2008 at 11:39 pm Leave a Comment

Kula Kulan Jifan Yunwa (Dan wake)

Dan wake daya ne daga cikin tarin abinciccikan gargajiya na  hausawa, saboda yadda yake yi wa yunwa rajamu ake yi masa take da “Kula kulan jifan yunwa

Yadda ake yin danwake:

1.     Farko dai za’a jika kanwa.

2.     Sannan a  samu garin fulawa, ko garin rogon dan wake a tankade

3.     Sai a tankade kuka ‘yar madaidaiciya a hada da wannanan tankadadden garin a tona su gaba daya

4.     Sai kuma a kawo waccan  jikakkiyar kanwa  a zuba a kai

5.     Sai a yi ta tonawa har sai ya hadu.

6.     Sannan a samu tukunya mai kyau a zuba ruwa a dora akan wuta har sai ya tafasa

7.     Sai a rinka diban wancen kwababben kulun ana gutsurar dai dai gwargwadon yadda ake so ana jefawa cikin wannan tafasashen ruwan

8.     Idan aka gama sai a bar shi ya yi ta tafasa, ana yi ana juyawa, a ba shi dan lokaci kadan

9.     Daga nan sai a rika tsamewa ana zubawa cikin wani ruwan daban mai sanyi ko mai dumi.

10.  Sannan  a samu abin suya a zuba mai – na na kuli, ko na ja-  sai a yanka yar albasa a ciki a soya 

11.Idan ya soyu sai a kwashe

12.Tuni dama an an tanadi dakakken yaji mara daddawa (mai fada, ko mara fada)

13.Sai a kwashe wannan danwaken, a tsane shi, sannan a zuba shi a kwano wankakke

14.Sannan a bade shi da yajin nan, kuma a dan bar bada gishiri, ko a marmasa magi

15.Daga nan kuma sai a zuba wannan soyayyen man

shaikenan danwake ya hadu, sai ci, amma kar a manta bisa al’ada shi dan wake hakkinsa shi ne a ci shi da tsinke ba da cokali ba, a ci lafiya, amma kar a manta da hankicin share gumi.

Hajiya Binta Lawan (Umma Imam) blabdallah@yahoo.com

Published in: on at 9:10 pm Leave a Comment

Neman Shawara 0001

Neman Shawara: Assalamu alaikum, da Allah ina son a taimakamin da shawara game da wata matsala da na samu kaina a ciki, kuma tana cimin tuwo a kwarya!

Yarinya ce da ni ‘yar shekara biyar take uzzuramin da kuka fiye da misali,

wani lokacin takan kai awa hudu tana kuka! har sai kaina ya yi ciwo,

in ta fara kuka ba ta dainawa sai an yi mata abin da take so,

wani lokacin in ta fara kuka da daddare ga shi dai ta data, amma sai an goya ta za ta yi shiru;  in ba haka ba sai ta kwana tana yi! Ta hana kowa bacci a gidan! 

Don Allah wace shawara za’a taimaka min da ita don maganin wannan matsala?

Published in: on at 1:00 pm Comments (2)

Hanyoyi 17 domin samun rayuwa mai albarka

Assalamu Alaikum warahmatullahi wa bara katuhuYana daga cikin abin da duk wani dan adam yake nema a rayuwarsa ta duniya, SAMUN ALABARKA; domin da haka ne zai samu rayuwa ingattacciya  mai cike da dimbin nasara da ci gaba, kuma hanya ce da za ta jawo wa ragowar iyalansa, da ma dukkan zurriyarsa samun albarka.Duba da mihimmancin wannan al’amari na ga dacewar in dan yi mana tsokaci game da abubuwan da suke sa mutum ya samu  albarka a rayuwarsa ta yau da kullum, dafatan Allah ya amfanar da mu, ya kuma datar da mu izuwa abin da ya ke shi ne dai dai .

Hanya ta Farko:  Fara komai da ambaton sunan Allah: Yana daga cikin abubuwan da suke jawo albarka a rayuwar mutum fara komai da ambaton sunan Allah, Manzon Allah (S.A.W) ya ce: Idan mutum ya shiga gidansa, yana mai ambaton Allah yayin shiga, da kuma lokacin cin abinci, shaidan  zai cewa abokansa:  “Ba ku da gurin kwana da kuma gurin cin abinci a yau”.Don haka ka ambaci sunan Allah; domin ambaton Allah shi ne abin da ya kamata musulmi ya yi kafin kowane aiki,  haka ma har a wurin tarawa da iyali, (jima’i) an so ka ambaci Allah kana mai cewa: ” Allahumma jannibnas-shaidana, wa jannibus-shaidana ma razaktana”, to idan Allah ya azurta su da da a wannan daren, to hakika zai albarkace shi, domin duk al’amarin da mabudinsa ambaton Allah ne, to kuwa albarka ba ta kaurace masa.

Zainab Jaafar Mahmud Adam

ummuaishatu@gmail.com 

Published in: on at 12:35 pm Leave a Comment

Kawalle ga ‘yan Nasihohi

Assalamu alaikum wa rahmatullahi.Farko dai Ina farin cikin da bude bangare na musamman a wannan shafi mai albarka, wanda zamu dinga haduwa da juna a cikinsa.

Ina yi wa ‘yan uwana yara nasiha wadda za ta amfane su insha Allah:

1-  Kiyaye yin salla a kan lokacinta; domin ita ce babbar ibada bayan kalmar shahada.

2-  Bin iyaye; domin hakkin yana da girma a musulunci, musamman iyaye mata.

3-  Kwazo a dukkanin karatuttuka musamman karatun Al’Kur’ani Mai girma; domin ilimi shi ne hasken rayuwar duniya da lahira. Jahili a cikin duhu yake duhu yake dundum!Wannan shi ne karshen nasihata a yau, sai wata haduwar.

Ma’assalama.

 Amina Muhd. Muslim (Ummi) shekara 10

Published in: on at 12:28 pm Leave a Comment