Tambaya ta 0001

Tambaya: Idan mace mai haila ta yi tsarki sai ta yi wanka bayan sallar asuba ta yi sallah kuma ta dauki azumin wannan ranar, shin za ta rama ko azuminta ya yi?

Amsa: Idan mace mai haila ta yi  tsarki kafin fitowar alfijir ko da da minti daya ne, amma dai ta tabbatar da tsarki, idan har a cikin Ramadan ne, to wajibi ne gare ta ta dauki azumi. kuma azuminta ya inganta ba sai ta rama ba,  domin ta yi azumi ne a cikin tsarki ko da kuwa ba ta yi wanka ba sai bayan fitowar alfijir, kamar yadda namiji idan janaba ta same shi ta hanyar jima’i ko mafarki, yake sahur ya dauki azumi, alhali bai yi wanka ba sai bayan fitowar alfijir kuma azumin sa ingantacce ne.Dangane da wannan, ina so in fadakar da mata game da wani al`amari shi ne idan haila ta zo wa mace, alhali ta yi azumin wannan rana; wasu mata suna zaton cewa, idan haila ta zo bayan an sha ruwa kafin ta ci wani abu, ko kuma bayan faduwar rana da kankanin lokaci cewa azumin ta ya karye. A`a azuminta yana nan, kuma ingantacce ne (ba sai ta rama ba).

Sheik Muhammad Sahel Al-Uthaimeen

Published in:  on February 6, 2008 at 11:11 pm Leave a Comment

The URI to TrackBack this entry is: http://iyalina.wordpress.com/2008/02/06/tambaya-ta-0001/trackback/

RSS feed for comments on this post.

Leave a Comment